Close Menu
PARADIGM NEWS
    Facebook X (Twitter) Instagram
    • Home
    • Privacy Policy
    Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
    PARADIGM NEWS
    • Home
    • Features

      The Untold Burden: Inside the Emotional Weight Nigeria’s Journalists Carry

      November 18, 2025

      Inside the Quiet Diplomacy Driving Plateau’s New Path to Peace

      November 16, 2025

      5 Key Facts About May Agbamuche-Mbu, Nigeria’s New INEC Boss

      October 8, 2025

      Happy Breadwinner A Story by Fatima Zahra Umar

      September 22, 2025

      Broken Rules, Unbroken Hearts Chapter One by Sadiya Datti

      September 21, 2025
    • News
      1. Local
      2. National
      3. International
      4. View All

      Parents, Two Children Killed as Mosquito Coil Sparks Inferno

      November 19, 2025

      UNICEF, Partners Launch Birth Registration Campaign in Gwarzo

      November 13, 2025

      Nasarawa LG Urges Residents to Register, Collect Voter Cards

      November 13, 2025

      Kano Community in Shock as Missing Nonagenarian Found Dead in Toilet Pit

      November 7, 2025

      Tinubu Sends Shettima to Kebbi, Orders Swift Rescue of Kidnapped Schoolgirls

      November 19, 2025

      Media Must Choose Hope Over Despair- Tinubu Charges Editors

      November 13, 2025

      Dr. Doro Assumes Office as Minister of Humanitarian Affairs

      November 12, 2025

      Nigeria Engages U.S. Through Diplomatic Channels to Ease Tensions- Minister

      November 12, 2025

      The Dakar Declaration on Health Sovereignty in Africa

      November 8, 2025

      Media Key to Health Sovereignty in Africa, REMAPSEN Tells Leaders at Galien Africa Forum 2025

      October 31, 2025

      Women Take Center Stage at Galien Africa Forum 2025

      October 30, 2025

      Young African Innovators Champion Health Sovereignty at 2025 Galien Africa

      October 30, 2025

      Kano Children Spotlight Cyber Violence, Edu Access in WCD Dialogue

      November 21, 2025

      Education Gulps Lion’s Share of Kano’s ₦1 Trillion 2026 Budget

      November 19, 2025

      Kano Online Chapel Hosts Workshop to Boost Credibility in Journalism

      November 19, 2025

      NASSI Launches Massive Pre-Retirement Training in Jigawa

      November 18, 2025
    • Politics

      Over 200 Serving, Former Kano Lawmakers Endorse Barau for 2027 Guber Race

      November 19, 2025

      Ringim Dismisses Reported Defection of Lawmaker, Others to APC

      November 15, 2025

      Former Kano Gov Shekarau Turns 70, Declares Lifelong Political Mission

      November 5, 2025

      PDP Re-elects Bello Suru as Chairman in Kebbi State

      September 30, 2025

      Online Reports False, I’ve Not Joined Any Party-Kwankwaso

      September 26, 2025
    • Conflict

      Natasha Livestreams Faceoff With Immigration Over Passport Seizure

      November 4, 2025

      Kebbi Gov’t Threatens Legal Action Against Malami Over Defamation Claims

      September 19, 2025

      FG Calls for Conflict-Sensitive Climate Adaptation to Tackle Insecurity

      September 3, 2025

      Kadpoly Retiree faults Committee, Demolition Of Property

      March 27, 2025

      President Tinubu Declares State of Emergency in Rivers State

      March 18, 2025
    • More
      • Analysis
      • Business
      • Crime
      • Cultural events
      • Economy
      • Education
      • Editorial
      • Entertainment
      • Environment
      • Fashion
      • Health
      • Lifestyle
      • Personality profile
      • Science
      • Sports
      • Technology
    • Hausa

      KSCHMA Ta Fara Tantance Masu Amfana da Shirin BHCPF a Kano

      November 11, 2025

      Allah Sarki! Ma’aikatan Wucin-gadi na Kafafen Yada Labarai

      November 6, 2025

      An Cafke Mutumin da yayi Garkuwa da ‘yayan dan’uwan sa a Bauchi

      October 27, 2025

      Rikici Ya Sa KNSG Rushe Hukumar Kare Masu Amfani da Kaya

      October 25, 2025

      Hisbah Ta Sanya Maiwushirya da ‘Yar Guda Cikin Auren Gata na Kano

      October 21, 2025
    Subscribe
    PARADIGM NEWS
    Home » Menene Tasirin Kafa Rundunar Tsaro Ta Jihar Kano?
    Hausa

    Menene Tasirin Kafa Rundunar Tsaro Ta Jihar Kano?

    EditorBy EditorJanuary 30, 2025Updated:January 30, 2025No Comments5 Mins Read
    Facebook Twitter Telegram WhatsApp
    FB IMG 1725344271069

    Tun bayan da majalisar dokokin jihar Kano ta sanar da yi wa ƙudurin kafa rundunar tsaro da gwamnatin jihar ta aike mata karatu na biyu, masana ke ta faman tsokaci dangane da hanyoyin da ya kamata a bi domin samun nasara.

    Turereniyar Karbar Abinci A Coci Ta Yi Sanadiyar Rayukan Mutane 10 A Abuja

    Kano dai na fama da matsaloli irin na rikice-rikicen dabanci da ƙwacen waya, lamarin da ya yi sanadiyar ajalin mutane da dama.

    Ad 4

    Ɗan majalisar dokoki mai wakiltar ƙaramar hukumar Ƙiru, Abubakar Tasi’u Ƙiru, na cikin ƴan majalisar da suke goyon bayan ƙudurin, inda ya lissafa wasu abubuwan da ke ƙunshe a cikin ƙudurin kamar haka.

    Ambasada Tatari Ya Mika Godiya Ga Wandanda Suka Halarci Nadin Sarautar Shi

    Kwamanda-Janar na jiha da ƙananan hukumomi ne za su jagoranci rundunar.

    Isa Kaita College

    Jami’an rundunar na da ikon kama masu laifi su hannunta su ga ƴansanda domin gurfanar da su a gaban hukuma.

    Jami’an rundunar na da damar amfani da bindigogi ƙirar gargajiya domin su kare kansu.

    Ash Noor

    Dakarun za su yi ƙoƙari domin kauce wa shiga harkokin siyasa, domin za a zuba waɗanda ba ƴansiyasa ba.

    Mun Samu Kasuwancin Magunguna na Kano a Rikice -Kwamishina

    Babu wanda za a ɗauka sai an tabbatar da nagartarsa da ingancinsa ba tun daga mahaifarsa, inda a cewarsa masu unguwanni da hakimai za su saka wa mutum hannu kafin a ɗauke shi domin gudun kar a ɗauki ɓatagari.

    A game da wannan yunƙurin na kafa rundunar tsaron, BBC ta tuntuɓi masanin harkokin tsaro, Auwal Bala Durumin Iya, inda ya ce abin farin ciki ne, amma ya kamata a yi abin da ya dace.

    Kwamishina Ya Mayar Wa Gwamnatin Kano Rarar Naira Miliyan Dari

    “Samar da rundunar tsaro ta jihar Kano abu ne mai kyau idan ka kalli irin laifuffukan da ake yi a Kano. Hakan ya sa gwamnati ta ga ya dace ta yi tsarin da ya kamata domin samar da jami’an tsaro da za su taimaka wa jami’an tsaro na gwamnati tarayya domin tabbatar da tsaro a jihar Kano.”

    Ya ce yanzu haka a nasa ɓangaren na masanin harkokin tsaro, yana gudanar da aikin horas da ƴan sa-kai daga ƙananan hukumomin Kano 44 domin koyar da su makamar aiki, domin su san yadda za su gudanar da aikin cikin ƙwarewa.

    A game da batun cewa Kano ba ta fama da barazanar tsaro ta ƴanbindiga, Durumin Iya ya ce kowace jiha na da matsalar da take fuskanta.

    Batagari Sun Yashe Asusun Ajiyar Kudin Wani Dan Kasuwa A Kano

    “Kowace jiha akwai matakin da ya kamata ta ɗauka domin kare ƴan jiharta. Saboda haka Kano na da maƙwabtaka da jihohin da suke fama da matsalolin tsaro, saboda haka ba laifi idan Kano ta ɗauki mataki kafin matsalar ta kawo gare ta. Idan gemun ɗan’uwanka ya kamata da wuta, sai ka shafa wa naka ruwa ne,” in ji shi.

    Sai dai ya ce akwai buƙatar a ɗauki waɗanda suka dace, kuma suke da ƙwarewa aiki da lungu da saƙon jihar.

    A game da fargabar amfani da jami’an tsaron da ake yunƙurin kafawa wajen amfani da su domin muzguna wa abokan hamayya domin cin ribar siyasa, Durumin Iya ya ce komai yana da amfani da rashin amfaninsa.

    MD Radio Kano Yace Sun Samun Nasarori Guda 60 a 2024

    “Amma amfanin samar da rundunar tsaron ya fi rashin amfaninsa. Ai ita gwamnati idan tana so ta yi amfani da jami’an tsaro, har na gwamnatin ma ana amfani da su. Kawai yana da kyau a zaƙulo waɗanda suka dace, sannan a tabbatar sun samu horo yadda ya dace.

    “Ƴan sa-kai su ne suka daɗe suna aikin tsaro. Su ya kamata a ɗauka, a ƙara musu horo bayan wanda muka musu domin a wayar musu da kai kan tsame aikinsu daga siyasa da addini da ƙabilanci da duk wani abu da zai zama cin zarafin ɗan’adam.”

    Ya ce ba za su zama kishiyar ƴansanda ba, kuma a cewarsa, ƴan sa-kai taimaka wa ƴansanda suke yi.

    “Su jami’an tsaron ne za su taimaka wa ƴansanda da bayanan sirri, sannan akwai wurare da dama da ƴansanda ba sa iya shiga, sai ƴan sa-kai ne za su shiga su kamo musu masu laifin su kai musu,” in ji shi, sannan ya ƙara da cewa idan aka samun haɗin kai tsakanin ƴan sa-kai da ƴansanda, lallai za a samu ɗa mai ido.

    Sai dai ya yi kira ga gwamnati da kada ta shigo da ƴansiyasa ciki lamarin, sannan ya yi kira ga ƴan jihar su ba jami’an tsaron goyon baya.

    “Idan aka samu haɗin kai tsakanin mutanen gari da ƴansanda da ƴan sa-kai ɗin, to lallai muna fata matsalolin da ake fuskanta a wasu jihohi ba za su ƙaraso Kano ba. Za a cigaba da gudanar da harkokin kasuwanci da ibada cikin lumana,” in ji Durumin Iya.

    BBC HAUSA

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

    Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram WhatsApp

    Related Posts

    KSCHMA Ta Fara Tantance Masu Amfana da Shirin BHCPF a Kano

    November 11, 2025

    Allah Sarki! Ma’aikatan Wucin-gadi na Kafafen Yada Labarai

    November 6, 2025

    An Cafke Mutumin da yayi Garkuwa da ‘yayan dan’uwan sa a Bauchi

    October 27, 2025

    Rikici Ya Sa KNSG Rushe Hukumar Kare Masu Amfani da Kaya

    October 25, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Editors Picks

    Kano Children Spotlight Cyber Violence, Edu Access in WCD Dialogue

    November 21, 2025

    AF 3.0: Expanded Nigeria ICC Endorses Biannual CSO Report

    November 19, 2025

    Over 200 Serving, Former Kano Lawmakers Endorse Barau for 2027 Guber Race

    November 19, 2025

    Education Gulps Lion’s Share of Kano’s ₦1 Trillion 2026 Budget

    November 19, 2025
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    Hajaj Albait 2
    © 2025 PARADIGM NEWS
    • Home
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.