Close Menu
PARADIGM NEWS
    Facebook X (Twitter) Instagram
    • Home
    • Privacy Policy
    Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
    PARADIGM NEWS
    • Home
    • Features

      How MH-NoW Advocates Reusable Pads for Nigerian Girls

      August 4, 2025

      I’ll dress elegantly for a week, lady vows as Kano women storm markets

      March 29, 2025

      Dr. Abdullahi Umar Ganduje’s Legacy of Progress and Excellence

      December 25, 2024

      The rise and fall of Faruk Lawan: A lesson in power and intrigues

      December 17, 2024

      Will The Axing of Zakirai Make Education Great In Kano

      December 17, 2024
    • News
      1. Local
      2. National
      3. International
      4. View All

      Kano Governor’s Aide Inspects N300m Projects in Minjibir LGA

      August 12, 2025

      Access to Next Funding Tranche Tied to Project Completion- KNSG Warns LGAs

      August 4, 2025

      Kano PWD Groups Deny Slamming Govt Over Disability Commission Delay

      July 31, 2025

      “Don’t Forget Us”- Spinal Cord Injury Survivors Call for Help in Kano

      July 31, 2025

      Journalists’ Pay, Healthcare Top Agenda as NUJ Pushes for Media Reform Bill

      August 13, 2025

      NUJ Tours Key Project Sites in Kano Ahead of NEC Meeting

      August 12, 2025

      FAAN Warns Against Unruly Passenger Behaviour at Airports

      August 11, 2025

      FG, U.S. Embassy Partner to Educate Nigerians on New Visa Rules

      August 9, 2025

      White House Defends Firing of BLS Director Amid Controversy

      August 4, 2025

      Israeli Attacks Kill 21 in Gaza; 181 Dead from Hunger

      August 4, 2025

      South Korea’s Lee Gains Public Backing After 15% US Tariff Deal

      August 4, 2025

      Trump to Withdraw U.S. from UNESCO Again, Slams “Woke”

      July 29, 2025

      Ondo Assembly Partners PROMAD to Track Public Projects

      August 13, 2025

      Major NDLEA Operation in Kano Nets 49 Suspects, Recovers Drugs

      August 13, 2025

      Kano Assembly Suspends Rano LGA Chairman for Three Months

      August 13, 2025

      Radda Showcases Bold Youth Empowerment Agenda in Katsina

      August 13, 2025
    • Politics

      Butchers, Livestock Traders Mobilise Funds for Tinubu, Namadi’s Re-Election

      August 8, 2025

      Kano APC Strategizes as Stakeholders Endorse Tinubu’s Re-Election

      August 6, 2025

      DSP Barau Jibrin Best to Lead Kano in 2027 – Minister Ata

      August 3, 2025

      Ex-NIMASA DG Jamoh Hints at Kaduna North Senatorial Ambition

      August 2, 2025

      Just in : Atiku Quits PDP, Blames Party’s New Direction

      July 16, 2025
    • Conflict

      Kadpoly Retiree faults Committee, Demolition Of Property

      March 27, 2025

      President Tinubu Declares State of Emergency in Rivers State

      March 18, 2025

      El-Rufai Defends Najaatu Muhammad Against Ribadus Denials

      February 5, 2025

      Tinubu’s Corruption Saga: Najaatu-Ribadu Feud Takes Center Stage

      February 5, 2025

      Kano Inaugurates Committee to Investigate Rimin Zakara Dispute

      February 3, 2025
    • More
      • Analysis
      • Business
      • Crime
      • Cultural events
      • Economy
      • Education
      • Editorial
      • Entertainment
      • Environment
      • Fashion
      • Health
      • Lifestyle
      • Personality profile
      • Science
      • Sports
      • Technology
    • Hausa

      Me yasa Harajin Karin Man Fetur na Kashi 5% Zai Kara Wahala

      August 13, 2025

      Yar Kasar Iran ta amsa laifin kashe mazaje 11 don mallakar dukiya

      August 12, 2025

      KNSG ta Bukaci Haɗin Kai Don Gina Hanyoyi, Wuta da Ruwan Sha a Kauyuka

      August 12, 2025

      KNSG Ta Yiwa Matasa 1,300 da Suka Daina Ta’addanci Afuwa

      August 12, 2025

      Abba Gida-Gida Ya Raba Kayan Sana’a Ga Matasa Sama da Dubu Ɗaya

      August 10, 2025
    Subscribe
    PARADIGM NEWS
    Home » Me yasa Harajin Karin Man Fetur na Kashi 5% Zai Kara Wahala
    Hausa

    Me yasa Harajin Karin Man Fetur na Kashi 5% Zai Kara Wahala

    EditorBy EditorAugust 13, 2025Updated:August 13, 2025No Comments5 Mins Read
    Facebook Twitter Telegram WhatsApp
    1755076702636

    Abba Dukawa

    A yanayi irin na Najeriya, inda matsalolin tattalin arziki da tsadar rayuwa suka yi kamari, karin haraji akan man fetur zai kara wa talakawa wahala me kawai.

    Sai dai masu tsara tattalin arzikin gwamnatin ba su nuna damuwa da yadda hakan zai shafi ‘yan kasa ba.

    Ad 4

    A gaskiya, shekaru biyun da suka gabata sun kasance shekaru na gwagwarmayar rayuwa ga mafi yawan ‘yan Najeriya.

    Dangote Ya Sanya Sunan Tinubu a Hanyar Shiga Matatar Man Fetur

    A fada a fili ba tare da boye gaskiya ba, manufofin tattalin arzikin gwamnatin Bola Tinubu na kara wa ‘yan kasa radadi. Cire tallafin man fetur da barin darajar Naira tana yawo da kanta sun haddasa tsananin talauci; miliyoyin iyalai na rasa abinci.

    Ad 3

    Tun daga ranar da Shugaba Bola Tinubu ya cire tallafin man fetur a ranar hawansa mulki (29 ga Mayu, 2023), tare da faduwar darajar Naira, ‘yan Najeriya suke fuskanci hauhawar farashi da ba ta da iyaka.

    A cikin wani rahoto da Financial Times ta fitar a ranar 16 ga Yuli, 2024, ta bayyana manufofin Tinubu da cewa “ba su da daidaito” kuma “idan ba a gyara ba, wannan tsarin wahalar da kai don samun sauki (shock therapy) zai ci tura.”

    Ash Noor

    Matatar Dangote Tayi Karin Kudin Man Fetur

    Dalilin da yasa Harajin Karin Man Fetur na Kashi 5% zai Kara Wahala:

    Al’umma har yanzu na cikin halin tsananin tsadar rayuwa, rashin tabbas na tattalin arziki da wahala.

    Saboda haka, kudurin gwamnatin na kara harajin kashi 5% akan man fetur da dizel, wanda za a fara aiwatarwa daga 1 ga Janairu, 2026, karkashin sabon dokar haraji, ba dai-dai ba ne kuma zalunci ne kai tsaye.

    Farashin abinci da sufuri Zai hauhawa matuka, haka kuma komai daga magani, kudin makaranta, layukan waya, har zuwa wutar lantarki. Ga jama’ar da ke cikin kunci, karin farashin man fetur da dizel tamkar yayyafa gishiri ne a kan rauni.

    A karkashin tsarin Tinubu, Naira ta rasa sama da kashi 60% na darajarta idan aka kwatanta da Dala. A ranar 31 ga Yuli, 2025, farashin lita daya na fetur ya kai N900, idan aka kwatanta da N187 kafin Tinubu ya hau mulki.

    Wannan sabon haraji zai ci gaba da raunana kasafin kudin iyalai, wanda tuni ya ruguje saboda tsadar man fetur da ke tasiri har kan farashin abubuwan bukata a gidajen Yan Kasa kamar shinkafa da kudin motar haya.

    Gwamnati na cewa wannan karin haraji zai taimaka wajen kara kudaden shiga daga bangaren da ba na man fetur ba da kuma dorewar tattalin arziki, amma hakan ba shi da tasiri idan aka duba yadda wannan mataki zai shafi iyalai, kananan ‘yan kasuwa, da ma’aikata.

    Daga dukkan alamu, gwamnatin Tinubu na nuna halin ko-in-kula da halin da mutane ke ciki – abin da ya kusa kama da rashin adalci.Gwamnati na ikirarin cewa tana ajiye $600 miliyan duk wata, kuma an kara kaso 40% a rabon kudade ga jihohi tun bayan cire tallafin fetur.

    To me ya sa ake kara wa ‘yan kasa haraji? Wannan sabanin manufar gyaran haraji ne da aka yi domin rage yawan haraji daban-daban.

    Duk da cewa gwamnatin na sa ran samun N796 biliyan daga wannan karin haraji, hakan na faruwa ne da radadin masu amfani da fetur da tuni ke fama da hauhawar farashi, karancin abinci da tsadar sufuri.

    Hujojin cewa wannan haraji zai taimaka wajen dorewar tattalin arziki ba su da karfi, musamman ganin cewa sauye-sauyen haraji da aka yi kwanan nan an yi su ne don kara yawan masu biyan haraji da dakile asarar kudaden shiga.

    A yayin da ake aiwatar da gyaran haraji, babu dalilin tunin rai ko na aikatawa da zai sa a kakaba sabon haraji kai-tsaye akan man da ake amfani da shi wajen sufuri.

    Gwamnatin da ke cewa “Sabon Fata” (Renewed Hope) ita ce manufarta, to wannan sabon haraji ya saba da alkawarin da ta dauka. Wannan harajin kuwa, cin amanar wannan alkawari ne kai tsaye.

    Idan gwamnati na son samun karin kudaden shiga daga bangaren man fetur, ya kamata ta saurari kiraye-kirayen da ke neman a rika bin diddigin kudade, a tilasta da’a a fannin kudi, tare da dakile kwaranyar kudade a kamfanin NNPC da sauran hukumomin da ke samar da kudaden shiga.

    Haka kuma, ya kamata ta kara yawan fitar da danyen mai da sayar da matatun da suka lalace.

    Gwamnatin “Sabon Fata” ya kamata ta zuba jari don fadada tattalin arzikin kasa domin karfafa fannonin kasuwanci da bunkasa ribar su. Ba daidai ba ne a dora nauyi a kan talakawa a sunan gyara.

    Saboda haka, gwamnatin ya kamata ta sake nazarin wannan haraji na kashi 5% akan man fetur, kuma a cire shi gaba daya daga dokar haraji.

    Jama’a sun riga sun nuna damuwa da cewa karin haraji akan man fetur zai kara tsadar rayiwu da kayayyaki – lamarin da zai kara tsananta halin da mutane ke ciki.

    Tuni wannan “Sabon Fata” ya koma “Sabon Fushi” domin miliyoyin mutane na fafutukar tsira da rayuwa. Ko albashin N70,000 da gwamnati ke biyan ma’aikata ba ya wadatar da su wajen sayen abubuwan bukata na yau da kullum.

    Dukawa ya rubuto daga Abuja kuma ana iya samunsa ta: abbahydukawa@gmail.com

    #Harajin 5 #Karin #Man Fetur
    Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram WhatsApp

    Related Posts

    Yar Kasar Iran ta amsa laifin kashe mazaje 11 don mallakar dukiya

    August 12, 2025

    KNSG ta Bukaci Haɗin Kai Don Gina Hanyoyi, Wuta da Ruwan Sha a Kauyuka

    August 12, 2025

    KNSG Ta Yiwa Matasa 1,300 da Suka Daina Ta’addanci Afuwa

    August 12, 2025

    Abba Gida-Gida Ya Raba Kayan Sana’a Ga Matasa Sama da Dubu Ɗaya

    August 10, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Editors Picks

    Ondo Assembly Partners PROMAD to Track Public Projects

    August 13, 2025

    Journalists’ Pay, Healthcare Top Agenda as NUJ Pushes for Media Reform Bill

    August 13, 2025

    Major NDLEA Operation in Kano Nets 49 Suspects, Recovers Drugs

    August 13, 2025

    Kano Assembly Suspends Rano LGA Chairman for Three Months

    August 13, 2025
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    Hajaj Albait 2
    © 2025 PARADIGM NEWS
    • Home
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.