Close Menu
PARADIGM NEWS
    Facebook X (Twitter) Instagram
    • Home
    • Privacy Policy
    Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
    PARADIGM NEWS
    • Home
    • Features

      The Untold Burden: Inside the Emotional Weight Nigeria’s Journalists Carry

      November 18, 2025

      Inside the Quiet Diplomacy Driving Plateau’s New Path to Peace

      November 16, 2025

      5 Key Facts About May Agbamuche-Mbu, Nigeria’s New INEC Boss

      October 8, 2025

      Happy Breadwinner A Story by Fatima Zahra Umar

      September 22, 2025

      Broken Rules, Unbroken Hearts Chapter One by Sadiya Datti

      September 21, 2025
    • News
      1. Local
      2. National
      3. International
      4. View All

      Parents, Two Children Killed as Mosquito Coil Sparks Inferno

      November 19, 2025

      UNICEF, Partners Launch Birth Registration Campaign in Gwarzo

      November 13, 2025

      Nasarawa LG Urges Residents to Register, Collect Voter Cards

      November 13, 2025

      Kano Community in Shock as Missing Nonagenarian Found Dead in Toilet Pit

      November 7, 2025

      Tinubu Sends Shettima to Kebbi, Orders Swift Rescue of Kidnapped Schoolgirls

      November 19, 2025

      Media Must Choose Hope Over Despair- Tinubu Charges Editors

      November 13, 2025

      Dr. Doro Assumes Office as Minister of Humanitarian Affairs

      November 12, 2025

      Nigeria Engages U.S. Through Diplomatic Channels to Ease Tensions- Minister

      November 12, 2025

      The Dakar Declaration on Health Sovereignty in Africa

      November 8, 2025

      Media Key to Health Sovereignty in Africa, REMAPSEN Tells Leaders at Galien Africa Forum 2025

      October 31, 2025

      Women Take Center Stage at Galien Africa Forum 2025

      October 30, 2025

      Young African Innovators Champion Health Sovereignty at 2025 Galien Africa

      October 30, 2025

      Education Gulps Lion’s Share of Kano’s ₦1 Trillion 2026 Budget

      November 19, 2025

      Kano Online Chapel Hosts Workshop to Boost Credibility in Journalism

      November 19, 2025

      NASSI Launches Massive Pre-Retirement Training in Jigawa

      November 18, 2025

      Media Is the Conscience of Society- Gov. Yusuf Tells Journalists at 2025 Retreat

      November 16, 2025
    • Politics

      Over 200 Serving, Former Kano Lawmakers Endorse Barau for 2027 Guber Race

      November 19, 2025

      Ringim Dismisses Reported Defection of Lawmaker, Others to APC

      November 15, 2025

      Former Kano Gov Shekarau Turns 70, Declares Lifelong Political Mission

      November 5, 2025

      PDP Re-elects Bello Suru as Chairman in Kebbi State

      September 30, 2025

      Online Reports False, I’ve Not Joined Any Party-Kwankwaso

      September 26, 2025
    • Conflict

      Natasha Livestreams Faceoff With Immigration Over Passport Seizure

      November 4, 2025

      Kebbi Gov’t Threatens Legal Action Against Malami Over Defamation Claims

      September 19, 2025

      FG Calls for Conflict-Sensitive Climate Adaptation to Tackle Insecurity

      September 3, 2025

      Kadpoly Retiree faults Committee, Demolition Of Property

      March 27, 2025

      President Tinubu Declares State of Emergency in Rivers State

      March 18, 2025
    • More
      • Analysis
      • Business
      • Crime
      • Cultural events
      • Economy
      • Education
      • Editorial
      • Entertainment
      • Environment
      • Fashion
      • Health
      • Lifestyle
      • Personality profile
      • Science
      • Sports
      • Technology
    • Hausa

      KSCHMA Ta Fara Tantance Masu Amfana da Shirin BHCPF a Kano

      November 11, 2025

      Allah Sarki! Ma’aikatan Wucin-gadi na Kafafen Yada Labarai

      November 6, 2025

      An Cafke Mutumin da yayi Garkuwa da ‘yayan dan’uwan sa a Bauchi

      October 27, 2025

      Rikici Ya Sa KNSG Rushe Hukumar Kare Masu Amfani da Kaya

      October 25, 2025

      Hisbah Ta Sanya Maiwushirya da ‘Yar Guda Cikin Auren Gata na Kano

      October 21, 2025
    Subscribe
    PARADIGM NEWS
    Home » Me yasa Harajin Karin Man Fetur na Kashi 5% Zai Kara Wahala
    Hausa

    Me yasa Harajin Karin Man Fetur na Kashi 5% Zai Kara Wahala

    EditorBy EditorAugust 13, 2025Updated:August 13, 2025No Comments5 Mins Read
    Facebook Twitter Telegram WhatsApp
    1755076702636

    Abba Dukawa

    A yanayi irin na Najeriya, inda matsalolin tattalin arziki da tsadar rayuwa suka yi kamari, karin haraji akan man fetur zai kara wa talakawa wahala me kawai.

    Sai dai masu tsara tattalin arzikin gwamnatin ba su nuna damuwa da yadda hakan zai shafi ‘yan kasa ba.

    Ad 4

    A gaskiya, shekaru biyun da suka gabata sun kasance shekaru na gwagwarmayar rayuwa ga mafi yawan ‘yan Najeriya.

    Dangote Ya Sanya Sunan Tinubu a Hanyar Shiga Matatar Man Fetur

    A fada a fili ba tare da boye gaskiya ba, manufofin tattalin arzikin gwamnatin Bola Tinubu na kara wa ‘yan kasa radadi. Cire tallafin man fetur da barin darajar Naira tana yawo da kanta sun haddasa tsananin talauci; miliyoyin iyalai na rasa abinci.

    Isa Kaita College

    Tun daga ranar da Shugaba Bola Tinubu ya cire tallafin man fetur a ranar hawansa mulki (29 ga Mayu, 2023), tare da faduwar darajar Naira, ‘yan Najeriya suke fuskanci hauhawar farashi da ba ta da iyaka.

    A cikin wani rahoto da Financial Times ta fitar a ranar 16 ga Yuli, 2024, ta bayyana manufofin Tinubu da cewa “ba su da daidaito” kuma “idan ba a gyara ba, wannan tsarin wahalar da kai don samun sauki (shock therapy) zai ci tura.”

    Ash Noor

    Matatar Dangote Tayi Karin Kudin Man Fetur

    Dalilin da yasa Harajin Karin Man Fetur na Kashi 5% zai Kara Wahala:

    Al’umma har yanzu na cikin halin tsananin tsadar rayuwa, rashin tabbas na tattalin arziki da wahala.

    Saboda haka, kudurin gwamnatin na kara harajin kashi 5% akan man fetur da dizel, wanda za a fara aiwatarwa daga 1 ga Janairu, 2026, karkashin sabon dokar haraji, ba dai-dai ba ne kuma zalunci ne kai tsaye.

    Farashin abinci da sufuri Zai hauhawa matuka, haka kuma komai daga magani, kudin makaranta, layukan waya, har zuwa wutar lantarki. Ga jama’ar da ke cikin kunci, karin farashin man fetur da dizel tamkar yayyafa gishiri ne a kan rauni.

    A karkashin tsarin Tinubu, Naira ta rasa sama da kashi 60% na darajarta idan aka kwatanta da Dala. A ranar 31 ga Yuli, 2025, farashin lita daya na fetur ya kai N900, idan aka kwatanta da N187 kafin Tinubu ya hau mulki.

    Wannan sabon haraji zai ci gaba da raunana kasafin kudin iyalai, wanda tuni ya ruguje saboda tsadar man fetur da ke tasiri har kan farashin abubuwan bukata a gidajen Yan Kasa kamar shinkafa da kudin motar haya.

    Gwamnati na cewa wannan karin haraji zai taimaka wajen kara kudaden shiga daga bangaren da ba na man fetur ba da kuma dorewar tattalin arziki, amma hakan ba shi da tasiri idan aka duba yadda wannan mataki zai shafi iyalai, kananan ‘yan kasuwa, da ma’aikata.

    Daga dukkan alamu, gwamnatin Tinubu na nuna halin ko-in-kula da halin da mutane ke ciki – abin da ya kusa kama da rashin adalci.Gwamnati na ikirarin cewa tana ajiye $600 miliyan duk wata, kuma an kara kaso 40% a rabon kudade ga jihohi tun bayan cire tallafin fetur.

    To me ya sa ake kara wa ‘yan kasa haraji? Wannan sabanin manufar gyaran haraji ne da aka yi domin rage yawan haraji daban-daban.

    Duk da cewa gwamnatin na sa ran samun N796 biliyan daga wannan karin haraji, hakan na faruwa ne da radadin masu amfani da fetur da tuni ke fama da hauhawar farashi, karancin abinci da tsadar sufuri.

    Hujojin cewa wannan haraji zai taimaka wajen dorewar tattalin arziki ba su da karfi, musamman ganin cewa sauye-sauyen haraji da aka yi kwanan nan an yi su ne don kara yawan masu biyan haraji da dakile asarar kudaden shiga.

    A yayin da ake aiwatar da gyaran haraji, babu dalilin tunin rai ko na aikatawa da zai sa a kakaba sabon haraji kai-tsaye akan man da ake amfani da shi wajen sufuri.

    Gwamnatin da ke cewa “Sabon Fata” (Renewed Hope) ita ce manufarta, to wannan sabon haraji ya saba da alkawarin da ta dauka. Wannan harajin kuwa, cin amanar wannan alkawari ne kai tsaye.

    Idan gwamnati na son samun karin kudaden shiga daga bangaren man fetur, ya kamata ta saurari kiraye-kirayen da ke neman a rika bin diddigin kudade, a tilasta da’a a fannin kudi, tare da dakile kwaranyar kudade a kamfanin NNPC da sauran hukumomin da ke samar da kudaden shiga.

    Haka kuma, ya kamata ta kara yawan fitar da danyen mai da sayar da matatun da suka lalace.

    Gwamnatin “Sabon Fata” ya kamata ta zuba jari don fadada tattalin arzikin kasa domin karfafa fannonin kasuwanci da bunkasa ribar su. Ba daidai ba ne a dora nauyi a kan talakawa a sunan gyara.

    Saboda haka, gwamnatin ya kamata ta sake nazarin wannan haraji na kashi 5% akan man fetur, kuma a cire shi gaba daya daga dokar haraji.

    Jama’a sun riga sun nuna damuwa da cewa karin haraji akan man fetur zai kara tsadar rayiwu da kayayyaki – lamarin da zai kara tsananta halin da mutane ke ciki.

    Tuni wannan “Sabon Fata” ya koma “Sabon Fushi” domin miliyoyin mutane na fafutukar tsira da rayuwa. Ko albashin N70,000 da gwamnati ke biyan ma’aikata ba ya wadatar da su wajen sayen abubuwan bukata na yau da kullum.

    Dukawa ya rubuto daga Abuja kuma ana iya samunsa ta: abbahydukawa@gmail.com

    #Harajin 5 #Karin #Man Fetur
    Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram WhatsApp

    Related Posts

    KSCHMA Ta Fara Tantance Masu Amfana da Shirin BHCPF a Kano

    November 11, 2025

    Allah Sarki! Ma’aikatan Wucin-gadi na Kafafen Yada Labarai

    November 6, 2025

    An Cafke Mutumin da yayi Garkuwa da ‘yayan dan’uwan sa a Bauchi

    October 27, 2025

    Rikici Ya Sa KNSG Rushe Hukumar Kare Masu Amfani da Kaya

    October 25, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Editors Picks

    AF 3.0: Expanded Nigeria ICC Endorses Biannual CSO Report

    November 19, 2025

    Over 200 Serving, Former Kano Lawmakers Endorse Barau for 2027 Guber Race

    November 19, 2025

    Education Gulps Lion’s Share of Kano’s ₦1 Trillion 2026 Budget

    November 19, 2025

    Parents, Two Children Killed as Mosquito Coil Sparks Inferno

    November 19, 2025
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    Hajaj Albait 2
    © 2025 PARADIGM NEWS
    • Home
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.