Najeriya ta sake fuskantar katsewar wutar lantarki sakamakon lalacewar babban layin lantarki na ƙasar a safiyar yau Asabar.

Lamarin da ya jefa miliyoyin mutane a jihohi da dama cikin duhu.

Wannan dai shi ne karo na uku da babban layin wutar ke lalacewa cikin mako ɗaya, kuma na takwas tun soma wannan shekara.

Bayanai daga aka tattara sun nuna cewa babu ko megawatt ɗaya a babban layin zuwa safiyar Asabar ɗin nan.

Masana kan harkar wutar lantarki dai sun yi kira da a sabunta kayayakin babbar cibiyar wutar lantaki ta ƙasar.

Sun ce yawan katsewar wutar lantarkin da ake fuskanta na da alaƙa ne da rashin sauya kayyakin babbar cibiyar wutar lantakin ƙasar.

 

 

 

 

 

 

Share.
Leave A Reply

Exit mobile version