Close Menu
PARADIGM NEWS
    Facebook X (Twitter) Instagram
    • Home
    • Privacy Policy
    Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
    PARADIGM NEWS
    • Home
    • Features

      I’ll dress elegantly for a week, lady vows as Kano women storm markets

      March 29, 2025

      Dr. Abdullahi Umar Ganduje’s Legacy of Progress and Excellence

      December 25, 2024

      The rise and fall of Faruk Lawan: A lesson in power and intrigues

      December 17, 2024

      Will The Axing of Zakirai Make Education Great In Kano

      December 17, 2024

      Harmattan Brings Boom to Tea, Noodle, Bean Cake Sellers in Kano

      December 15, 2024
    • News
      1. Local
      2. National
      3. International
      4. View All

      Gaya Emirate Withdraws Traditional Title Of Wazirin Gaya From Alhaji Usman Alhaji

      June 19, 2025

      KNSG, Communities Hold Consultative Meeting Over Taludu Flyover

      June 14, 2025

      Alliance of ’91’ Old Boys’ Welfare Packages Uplift Local Communities

      June 10, 2025

      Eid: Dangote Cement Strengthens Govt-Community Ties in Kogi

      June 8, 2025

      Tinubu Hails Kaduna’s Development Efforts, Pledges More Support

      June 20, 2025

      We’ll Never Allow Re-looting of Recovered Assets Again – EFCC Chair

      June 19, 2025

      Nigeria Deepens Bilateral Ties with China on Academic Culture

      June 19, 2025

      Minister Warns Against Fake News, Praises GOCOP’s Integrity

      June 18, 2025

      Nigeria Showcases Bold Health Reforms at BRICS, Pledges $200M

      June 19, 2025

      KSrelief to Tackle Nigeria’s Water Shortage with 78 Solar Boreholes

      June 19, 2025

      NYC Comptroller Arrested During ICE Protest At Manhattan Court

      June 17, 2025

      REMAPSEN @ 5: President Calls for Stronger Media Action on Health, Climate

      June 13, 2025

      Kano Unveils Safe Corridor to End Youth Thuggery,Political Violence

      June 20, 2025

      FUDECO, SPARC Call For Urgent Reforms To Support Pastoralist Communities In Kaduna

      June 18, 2025

      Kano to Host Natl Summit on Creative Industry to Boost Nigeria’s GDP

      June 17, 2025

      Kano Online Chapel Begins Membership Registration for Digital Media Professionals

      June 17, 2025
    • Politics

      Ringim Faults Sule Lamido’s Claims in Newly Launched Autobiography

      June 20, 2025

      Makinde 2027: Presidential Campaign Posters Flood Jigawa

      June 19, 2025

      How Chaos Erupts at APC Meeting Over Shettima Snub in Tinubu’s Endorsement Bid

      June 16, 2025

      North East APC Forum Endorses Tinubu/Kashim Ticket for 2027

      June 16, 2025

      APC Is Ready to Welcome You Anytime: Tinubu Tells Wike

      June 16, 2025
    • Conflict

      Kadpoly Retiree faults Committee, Demolition Of Property

      March 27, 2025

      President Tinubu Declares State of Emergency in Rivers State

      March 18, 2025

      El-Rufai Defends Najaatu Muhammad Against Ribadus Denials

      February 5, 2025

      Tinubu’s Corruption Saga: Najaatu-Ribadu Feud Takes Center Stage

      February 5, 2025

      Kano Inaugurates Committee to Investigate Rimin Zakara Dispute

      February 3, 2025
    • More
      • Analysis
      • Business
      • Crime
      • Cultural events
      • Economy
      • Education
      • Editorial
      • Entertainment
      • Environment
      • Fashion
      • Health
      • Lifestyle
      • Personality profile
      • Science
      • Sports
      • Technology
    • Hausa

      Sabuwar Daraktar Harkokin Ma’aikata Ta Gwarzo Ta Kama Aiki

      June 20, 2025

      Kano Ta Kaddamar da Shirin Dasa Itatuwa Don Yaki da Hamada

      June 18, 2025

      Dangote Ya Sanya Sunan Tinubu a Hanyar Shiga Matatar Man Fetur

      June 7, 2025

      NAHCON Ta Tabbatar da Tsaro Bayan Gobara a Masaukin Alhazai

      June 7, 2025

      Sarki Sanusi Ya Umarci Hakimai Su Shigo Kano Yin Hawan Sallah

      June 3, 2025
    Subscribe
    PARADIGM NEWS
    Hausa

    Kano a Shirye Take ta Yaki Kwalara da Sauran Cututtuka – KNCDC

    EditorBy EditorJune 26, 2024Updated:August 7, 2024No Comments3 Mins Read
    Facebook Twitter Telegram WhatsApp
    IMG 20240626 WA0105

    Biyo bayan shawarwarin da Kwamishinan Lafiya na Jihar Kano ya bayar kan yadda al’ummar jihar Kano za su yi ta’ammali da ruwan sama, Cibiyar Daƙile Cututtuka Masu Yaɗuwa ta Jihar Kano (KNCDC) ita ma ta bayar da shawarwarin yadda mutane za su kare kansu daga kamuwa da cutar ta kwalara.

    Darakta Janar na Cibiyar, Farfesa Muhammad Abbas ya ja hankalin al’ummar jihar Kano da kada su ɗauki lamarin cutar kwalara da wasa, saboda mummunan abin da take tattare da shi ga al’umma.

    RELATED: KNHA Passes Kano State Centre For Disease Control Bill 2024

    Ad 4

    A wata sanarwar manema labarai da ta fito daga Sashin Hulɗa da Jama’a na Ma’aikatar Lafiya ta hakaito Farfesa Abbas yana cewa kwalara ta kasance abar sanya firgici a jihohi da yawa na wannan ƙasa, don haka, duk da cewa har yanzu babu cutar a jihar Kano, ana kira da babbar murya ga jama’ar jihar da su ɗauki matakan kuɓutar da jihar daga wannan mummunar cuta.

    Darakta Janar ɗin ya bayyana cewa sanannun alamun kamuwa da cutar sun haɗa da gudawa, da amai da kuma saurin ƙarewar ruwa a jikin mutum, yana mai bayar da shawarar cewa duk wanda aka ga yana ɗauke da ɗaya ko dukkan alamomin a hanzarta kai shi asibiti mafi kusa.

    Farfesa Abbas ya jaddada cewa wajibi mutane su ɗauki matakan gaggawa na hana ɓarkewar kwalara a jihar nan ta hanyar yawaita wanke hannu da ruwa da sabulu, da shan ruwa mai tsafta, da nesantar gurɓatattun hanyoyin samun ruwa da suka haɗa ruwan sama mara kyau.

    Ad 3

    Sauran, in ji shi, sun haɗa da gujewa haɗuwa da wanda ya nuna alamar yana ɗauke da cutar, da ajiye abinci yadda ya dace da kuma wanke hannaye kafin da bayan fitowa daga banɗaki.

    Darakta Janar ɗin ya kuma jaddada cewa mutane su rinƙa kasancewa a cikin tsafta a wani mataki na ƙara ɗaukar matakan kariya daga kwalara, tare da yin amfani da banɗaki yadda ya kamata, da zubar da shara a inda ya dace, da kuma wanke da ruwa da sabulu hannu kafin da bayan an ci abinci.

    Ya ce, lallai a dafa abinci ya dahu sosai sannan a ajiye shi yadda ya kamata, a guji ɗanye da dafaffen naman ruwa, sannan a tabbatar an wanke kayan lambu da na marmari da ruwa mai tsafta kafin a yi amfani da su.

    Ya tabbatar wa al’ummar Kano da cewa cibiyar tasa tana ta ƙoƙarin, bisa cikakken goyon bayan da yake samu da ma’aikatar lafiya, wajen mayar da hankali kan duk wata cuta da za ta haifar da matsala ga zamantakewa da walwalar mutanen Kano.

    “Ina amfani da wannan damar wajen taya Gwamnan lafiya, Alhaji Abba Kabir Yusuf murnar cika shekara ɗaya a karagar mulki. Haƙiƙa, salon mulkinka, yana sanya mana karsashi, sannan kulawar da ka bai wa sashin lafiya tana da ƙayarwa ainun.

    “Ina kuma miƙa godiyata ga Kwamishinan Lafiya, Dakta Abubakar Labaran Yusuf saboda jajircewarsa wajen ganin an cika ƙudurorin da mai girma Gwamna yake da su a ɓangaren lafiya, da kuma sanya mu, mu shugabannin hukumomin lafiya, a hanya da yake yi”, Farfesa Abbas ya ƙarƙare.

    Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram WhatsApp

    Related Posts

    Sabuwar Daraktar Harkokin Ma’aikata Ta Gwarzo Ta Kama Aiki

    June 20, 2025

    Kano Ta Kaddamar da Shirin Dasa Itatuwa Don Yaki da Hamada

    June 18, 2025

    Dangote Ya Sanya Sunan Tinubu a Hanyar Shiga Matatar Man Fetur

    June 7, 2025

    NAHCON Ta Tabbatar da Tsaro Bayan Gobara a Masaukin Alhazai

    June 7, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Editors Picks

    ZDLH CoP Urges Parents in Sokoto to Prioritize Child Immunization

    June 21, 2025

    ZDLH Scorecard Unveiled: Bauchi Steps Up Fight Against Zero-Dose

    June 21, 2025

    ZDLH CoP in Borno Spurs Action on Sustainable Immunization Funding

    June 21, 2025

    Meet Mr. Enitan: The Driving Force Behind Nigeria’s Edu Sector

    June 20, 2025
    Hajaj Albait 2
    © 2025 PARADIGM NEWS
    • Home
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.