Close Menu
PARADIGM NEWS
    Facebook X (Twitter) Instagram
    • Home
    • Privacy Policy
    Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
    PARADIGM NEWS
    • Home
    • Features

      How MH-NoW Advocates Reusable Pads for Nigerian Girls

      August 4, 2025

      I’ll dress elegantly for a week, lady vows as Kano women storm markets

      March 29, 2025

      Dr. Abdullahi Umar Ganduje’s Legacy of Progress and Excellence

      December 25, 2024

      The rise and fall of Faruk Lawan: A lesson in power and intrigues

      December 17, 2024

      Will The Axing of Zakirai Make Education Great In Kano

      December 17, 2024
    • News
      1. Local
      2. National
      3. International
      4. View All

      Kano Invests N300 Million in Sumaila LGA to End Water Crisis

      August 14, 2025

      Kano Governor’s Aide Inspects N300m Projects in Minjibir LGA

      August 12, 2025

      Access to Next Funding Tranche Tied to Project Completion- KNSG Warns LGAs

      August 4, 2025

      Kano PWD Groups Deny Slamming Govt Over Disability Commission Delay

      July 31, 2025

      FG Pledges Timely Completion of Enugu-Port Harcourt Expressway

      August 15, 2025

      South East Projects in Focus as FG Begins Citizens’ Engagement

      August 14, 2025

      Journalists’ Pay, Healthcare Top Agenda as NUJ Pushes for Media Reform Bill

      August 13, 2025

      NUJ Tours Key Project Sites in Kano Ahead of NEC Meeting

      August 12, 2025

      White House Defends Firing of BLS Director Amid Controversy

      August 4, 2025

      Israeli Attacks Kill 21 in Gaza; 181 Dead from Hunger

      August 4, 2025

      South Korea’s Lee Gains Public Backing After 15% US Tariff Deal

      August 4, 2025

      Trump to Withdraw U.S. from UNESCO Again, Slams “Woke”

      July 29, 2025

      WHD: AMG Foundation Commits ₦25M to Kano Humanitarian Trust Fund

      August 19, 2025

      Katsina Govt Promises Children’s Inclusion in Decision-making

      August 16, 2025

      Ondo Assembly Partners PROMAD to Track Public Projects

      August 13, 2025

      Major NDLEA Operation in Kano Nets 49 Suspects, Recovers Drugs

      August 13, 2025
    • Politics

      NNPP Alleges Collusion, Rejects Tsanyawa/Ghari Rerun Results

      August 17, 2025

      Kano Bye-Election: PDP Demands Transparency, Rejects Intimidation of Voters

      August 16, 2025

      Butchers, Livestock Traders Mobilise Funds for Tinubu, Namadi’s Re-Election

      August 8, 2025

      Kano APC Strategizes as Stakeholders Endorse Tinubu’s Re-Election

      August 6, 2025

      DSP Barau Jibrin Best to Lead Kano in 2027 – Minister Ata

      August 3, 2025
    • Conflict

      Kadpoly Retiree faults Committee, Demolition Of Property

      March 27, 2025

      President Tinubu Declares State of Emergency in Rivers State

      March 18, 2025

      El-Rufai Defends Najaatu Muhammad Against Ribadus Denials

      February 5, 2025

      Tinubu’s Corruption Saga: Najaatu-Ribadu Feud Takes Center Stage

      February 5, 2025

      Kano Inaugurates Committee to Investigate Rimin Zakara Dispute

      February 3, 2025
    • More
      • Analysis
      • Business
      • Crime
      • Cultural events
      • Economy
      • Education
      • Editorial
      • Entertainment
      • Environment
      • Fashion
      • Health
      • Lifestyle
      • Personality profile
      • Science
      • Sports
      • Technology
    • Hausa

      An Cafke Ma’aikaciyar jinya ta bogi bayan ta Kula da Marasa lafiya 4,400

      August 18, 2025

      Gwamnatin Imo ta Haramta bikin yaye Daliban Nursery da JSS 3

      August 18, 2025

      Malam Ali ya samu injin faci daga Dan Majalisar Fagge bayan kuka a kafafen sada zumunta

      August 18, 2025

      Me yasa Harajin Karin Man Fetur na Kashi 5% Zai Kara Wahala

      August 13, 2025

      Yar Kasar Iran ta amsa laifin kashe mazaje 11 don mallakar dukiya

      August 12, 2025
    Subscribe
    PARADIGM NEWS
    Home » Nuhu Ribadu Ya Musanta Zargin Da Nijar Ke Yi Akan Nageria
    Hausa

    Nuhu Ribadu Ya Musanta Zargin Da Nijar Ke Yi Akan Nageria

    EditorBy EditorDecember 28, 2024Updated:December 28, 2024No Comments5 Mins Read
    Facebook Twitter Telegram WhatsApp
    1735385597825

    Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro Malam Nuhu Ribaɗu, ya nuna takaicinsa kan wasu zarge zarge, da shugaban mulkin sojin Nijar Janar Abdulrahman Tchiani ya yi yayin hirarsa da kafar talabijin ɗin kasar ranar Laraba.

    Minister receives Kaduna Abducted Journalists salutes NSA

    Shi dai Janar Tchiani ya zargi Najeriya da ba ƙasar Faransa hadin kai wajen ba ƴan bindiga mafaka da kuma ƙoƙarin kafa sansani a arewacin Najeriya, don shirya yadda za su farwa ƙasarsa.

    Ad 4

    To sai dai a hirarsa da BBC Hausa, mai ba Shugaban Najeriyar shawara kan sha’anin tsaro Malam Nuhu Ribadu, ya ce dukkan wadannan maganganu basu da tushe, ballantana makama, kana Najeriya ba za ta taba yi wa Nijar zagon kasa ko ta bari wata masifa ta auka mata ba.

    Northern Star Youth Initiative Kicks Against Nigeria’s Romance With France

    Ya ce ‘’Ko Ingila da ta mulki Najeriya ba ta taɓa kawo sojoojinta kasarmu ba, sai da suka yi dukkan mai yiwuwa muka ƙi yarda sannan suka kai su Nijar din, ita kuma ta yadda ta karɓa, haka ita ma Faransar da ta mulke su ta so ta kawo mana sojojinta, muka ce ba mu amince ba, me ya sa sai yanzu za mu sake shawara?

    Ad 3

    Sai dai a cewarsa ya kamata shugabannin Nijar din su fahimci cewa don kawai suna da wata matsala da Faransa, ba shi ke nufin cewa dole ne ita ma Najeriya ta yi zaman doya da manja da kasar ba.

    Wani babban zargi da shugaban Nijar din ya yi wa Najeria shine na ba wa sojojin Faransar sansani a wani tsbiri a jihar Borno, daf da tafkin Chadi, da ake kira Canada, inda Faransar ta jibge sojojinta a wurin, har ma ya kama sunan shi Nuhu Ribadu, ya ce ya san duk wannan magana

    Ash Noor

    Sai dai a hirarsa da BBC, Nuhu Ribadu, ya ce ‘’Ba shakka shi shugaban Nijar ya san Najeriya sosai, amma ina so ku a matsayinku na ƴan jarida, ku je wuraren da ya faɗa ku duba da kanku, ko ku tambayi mazauna wuraren ko akwai wasu baƙi ma, ballantana sojojin wasu ƙasashen’’

    ‘’Su shugabannin mulkin sojin Nijar ya kamata su fahimci cewa mu Najeriya ba matsala bane gare su, waɗannan yan ta’adda da duka muke yaki da su sune matsalarmu, ya kamata mu tunkare su tare’’ in ji mai ba wa shugaban Najeriyar shawara kan harkokin tsaro.

    Ya kara da cewa ‘’Don Allah shugabannin Nijar su sake dubawa, ba yadda za a yi a ce Najeriya ce za ta taimaka wa yan ta’adda su yake ta, kuma ya kamata su san cewa idan sun kori Faransa sun kuma sake kawo wasu, to sun canja matsalar ne kawai, bai kamata su kawo wasu ba, duk wanda ya zo maka da farko zai zo a matsayin aboki ne, ko lokacin da suka kawo Faransa mun ba su wannan shawarar, amma basu ɗauka ba’’

    Ya ce Najeriya ba ta da niyyar nesanta kanta da maƙwabciyar ta ta, domin kasashen biyu da al’umominsu yan uwan juna ne, don haka kamata ya yi su hada kai su yi aiki tare, don ci gaban al’umominsu.

    A baya bayan nan ma sai da ministan harkokin wajen Nijar ɗin ya gayyaci jami’a mai kula da harkokin diflomasiyya a ofishin jakadancin Najeriya da ke ƙasar, don ta je ta yi bayani kan zargin da suke yi wa Najeriyar na hada kai da wasu kasashen Turai wajen shirya mata manaƙisa.

    Ministan ya yi zargi cewa, duk da irin na-mijin ƙoƙarin da Nijar ke ta yi na ganin ta kyautata dangantaka da daɗaɗɗiyar aminiya ko ma abokiyar tagwaitakar ta ta, watau Najeriya, amma ƙasar bata hakura ba, inda take ci gaba da haɗa kai da wasu manyan ƙasashen duniya da jami’an tsohuwar gwamnatin Bazoum da ke zaman mafaka a Najeryar ake ci gaba da kitsa yadda za a jefa ƙasar cikin hargitsi.

    Zarge zargen da shugaban Nijar ya yi wa Najeriya

    Shugaban na mulkin sojin Nijar ya ce daga bayanan da suka samu a daɗewa sun fahimci cewa na shirin kafa sansanin Lakurawa a wani daji da ke jihohin Sokoto da Zamfara da kuma Kebbi.

    ‘’Wasu manyan ‘yanta’adda da muka kama, sun shaida mana cewa a ranar 4 ga watan Maris ɗin shekarar 2024, Faransa ta ƙulla wata yarjejeniya da mayaƙan ISWAP, kuma shugabannin Najeriya na sane da ita, cewa za a mayar da dajin Gaba da ke jihohin Sokoto da Zamfara da Kebbi a Najeriya sansanin horas da mayaƙan Lakurawa’’, in ji shugaban na Nijar.

    Janar Tchiani ya yi zargin cewa an tanadin sansanin ne domin horas da mayaƙan Lakura don su watsu a jihohin Sokoto da Zamfara da kuma jihar Kebbi da kuma jamhuriyar Nijar.

    Shugaban na Nijar ya ce duk da iƙirarin mayaƙan da suka kama suka na cewa jagororin Najeriya na sane, ba su yarda da maganar ‘yan bindigar ba.

    Haka ma shugaban na Nijar ya zargi mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu da masaniya game da wannan batu.

    Yayin zargin cewa an ƙuduri aniyar horas da Lakurawan ne domin su kawo tarnaƙi ga aikin bututun man ƙasar da ka shimfiɗa zuwa Jamhuriyar Benin mai makwabtaka.

    Janar Tchiani ya zargi ƙasashe makwabtan Nijar da bai wa Faransa damar kafa sansanoni a ƙasashen domin horas da ‘yanta’adda da niyyar yaƙar Nijar.

    A baya-bayan nan dai dangantaka tsakanin Najeriya da Nijar na ci gaba da yin tsami, ko a makon da ya gabata ma gwamnatin mulkin sojin Nijar ɗin ta zargi Najeriya da shirya mata maƙarƙashiya, kodayake gwamnatin Najeriya ta musanta zargin.

    BBC HAUSA

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

    Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram WhatsApp

    Related Posts

    An Cafke Ma’aikaciyar jinya ta bogi bayan ta Kula da Marasa lafiya 4,400

    August 18, 2025

    Gwamnatin Imo ta Haramta bikin yaye Daliban Nursery da JSS 3

    August 18, 2025

    Malam Ali ya samu injin faci daga Dan Majalisar Fagge bayan kuka a kafafen sada zumunta

    August 18, 2025

    Me yasa Harajin Karin Man Fetur na Kashi 5% Zai Kara Wahala

    August 13, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Editors Picks

    WHD: AMG Foundation Commits ₦25M to Kano Humanitarian Trust Fund

    August 19, 2025

    RMNCAH Takes Center Stage as ISMPH Engender Health Trains Kano Media Influencers

    August 19, 2025

    RMAFC to Adopt Data-Driven Approach in Revenue Sharing Review

    August 19, 2025

    KNSG Inaugurates Committee to Tackle Out-of-School Children

    August 19, 2025
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    Hajaj Albait 2
    © 2025 PARADIGM NEWS
    • Home
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.