Close Menu
PARADIGM NEWS
    Facebook X (Twitter) Instagram
    • Home
    • Privacy Policy
    Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
    PARADIGM NEWS
    • Home
    • Features

      I’ll dress elegantly for a week, lady vows as Kano women storm markets

      March 29, 2025

      Dr. Abdullahi Umar Ganduje’s Legacy of Progress and Excellence

      December 25, 2024

      The rise and fall of Faruk Lawan: A lesson in power and intrigues

      December 17, 2024

      Will The Axing of Zakirai Make Education Great In Kano

      December 17, 2024

      Harmattan Brings Boom to Tea, Noodle, Bean Cake Sellers in Kano

      December 15, 2024
    • News
      1. Local
      2. National
      3. International
      4. View All

      KNSG Launches Safe Space for Women Battling Drug Addiction

      July 22, 2025

      Rescue Efforts End in Tragedy as Four Drown in Kano Waterway

      July 19, 2025

      Kano Assembly Denies Investigating ALGON Chair Hajiya Sa’adatu

      July 18, 2025

      Kano Unveils N69B Dev Package Covering Roads, Education, Health

      July 12, 2025

      Renewed Hope Estate Kano Set for Tinubu’s Commissioning

      July 25, 2025

      Empower Youth to Drive Natl Development — NPC Tells Nigerians

      July 25, 2025

      Babangida, Rikiji, Somefun, Inuwa Among Key Appointees in Tinubu’s July Reshuffle

      July 18, 2025

      SPESSE Workshop Equips Nigerian Officials to Address GBV

      July 11, 2025

      Just in: Saudi Arabia’s Sleeping Prince Dies After 19 Years in Coma

      July 20, 2025

      REMAPSEN–Galien Africa Partnership to Strengthen Africa’s Health Communication, Climate Resilience

      July 18, 2025

      Alliance Rights and Health Rallies Africa to Deliver on Gender Justice

      July 12, 2025

      NNPC Pushes for Sustainable Energy Vision at Global OPEC Stage

      July 10, 2025

      Kano Transport Commissioner Pulls Out as Surety in Drug Case

      July 26, 2025

      Make Every Naira Count for Children in Upcoming Budget-UNICEF to KNSG

      July 23, 2025

      KNSG Vows Increased Support for Radio Kano

      July 22, 2025

      75 CSOs Back Kano’s War on Youth Crime and Drug Abuse

      July 22, 2025
    • Politics

      Just in : Atiku Quits PDP, Blames Party’s New Direction

      July 16, 2025

      Sule Lamido Backs Opposition Coalition Under ADC

      July 15, 2025

      Ringim Blames Sule Lamido, Not Wike, for PDP Crisis

      July 13, 2025

      Commissioner Waiya Endorses Women’s Political Representation

      July 7, 2025

      Gauta Club Gets 14 New Patrons as Waiya Champions Inclusive Politics

      July 5, 2025
    • Conflict

      Kadpoly Retiree faults Committee, Demolition Of Property

      March 27, 2025

      President Tinubu Declares State of Emergency in Rivers State

      March 18, 2025

      El-Rufai Defends Najaatu Muhammad Against Ribadus Denials

      February 5, 2025

      Tinubu’s Corruption Saga: Najaatu-Ribadu Feud Takes Center Stage

      February 5, 2025

      Kano Inaugurates Committee to Investigate Rimin Zakara Dispute

      February 3, 2025
    • More
      • Analysis
      • Business
      • Crime
      • Cultural events
      • Economy
      • Education
      • Editorial
      • Entertainment
      • Environment
      • Fashion
      • Health
      • Lifestyle
      • Personality profile
      • Science
      • Sports
      • Technology
    • Hausa

      San Makwabciyarka Ta Hade Hannu da Majalisar Malamai

      July 24, 2025

      Gwamnatin Kano Ta Raba Takin Zamani Ga Manoma a Gwarzo

      July 22, 2025

      Halin Da Gwamnan Katsina Ke Ciki Bayan Hatsarin Mota

      July 21, 2025

      Kwamitin Gasar Karatun Alkur’ani Ya Koka da Zargin Almundahana

      July 21, 2025

      Buhari Jagora Ne Mai Kaunar Kasar Nageria-In Ji Gwamnan Kano

      July 14, 2025
    Subscribe
    PARADIGM NEWS
    Home » Nuhu Ribadu Ya Musanta Zargin Da Nijar Ke Yi Akan Nageria
    Hausa

    Nuhu Ribadu Ya Musanta Zargin Da Nijar Ke Yi Akan Nageria

    EditorBy EditorDecember 28, 2024Updated:December 28, 2024No Comments5 Mins Read
    Facebook Twitter Telegram WhatsApp
    1735385597825

    Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro Malam Nuhu Ribaɗu, ya nuna takaicinsa kan wasu zarge zarge, da shugaban mulkin sojin Nijar Janar Abdulrahman Tchiani ya yi yayin hirarsa da kafar talabijin ɗin kasar ranar Laraba.

    Minister receives Kaduna Abducted Journalists salutes NSA

    Shi dai Janar Tchiani ya zargi Najeriya da ba ƙasar Faransa hadin kai wajen ba ƴan bindiga mafaka da kuma ƙoƙarin kafa sansani a arewacin Najeriya, don shirya yadda za su farwa ƙasarsa.

    Ad 4

    To sai dai a hirarsa da BBC Hausa, mai ba Shugaban Najeriyar shawara kan sha’anin tsaro Malam Nuhu Ribadu, ya ce dukkan wadannan maganganu basu da tushe, ballantana makama, kana Najeriya ba za ta taba yi wa Nijar zagon kasa ko ta bari wata masifa ta auka mata ba.

    Northern Star Youth Initiative Kicks Against Nigeria’s Romance With France

    Ya ce ‘’Ko Ingila da ta mulki Najeriya ba ta taɓa kawo sojoojinta kasarmu ba, sai da suka yi dukkan mai yiwuwa muka ƙi yarda sannan suka kai su Nijar din, ita kuma ta yadda ta karɓa, haka ita ma Faransar da ta mulke su ta so ta kawo mana sojojinta, muka ce ba mu amince ba, me ya sa sai yanzu za mu sake shawara?

    Ad 3

    Sai dai a cewarsa ya kamata shugabannin Nijar din su fahimci cewa don kawai suna da wata matsala da Faransa, ba shi ke nufin cewa dole ne ita ma Najeriya ta yi zaman doya da manja da kasar ba.

    Wani babban zargi da shugaban Nijar din ya yi wa Najeria shine na ba wa sojojin Faransar sansani a wani tsbiri a jihar Borno, daf da tafkin Chadi, da ake kira Canada, inda Faransar ta jibge sojojinta a wurin, har ma ya kama sunan shi Nuhu Ribadu, ya ce ya san duk wannan magana

    Ash Noor

    Sai dai a hirarsa da BBC, Nuhu Ribadu, ya ce ‘’Ba shakka shi shugaban Nijar ya san Najeriya sosai, amma ina so ku a matsayinku na ƴan jarida, ku je wuraren da ya faɗa ku duba da kanku, ko ku tambayi mazauna wuraren ko akwai wasu baƙi ma, ballantana sojojin wasu ƙasashen’’

    ‘’Su shugabannin mulkin sojin Nijar ya kamata su fahimci cewa mu Najeriya ba matsala bane gare su, waɗannan yan ta’adda da duka muke yaki da su sune matsalarmu, ya kamata mu tunkare su tare’’ in ji mai ba wa shugaban Najeriyar shawara kan harkokin tsaro.

    Ya kara da cewa ‘’Don Allah shugabannin Nijar su sake dubawa, ba yadda za a yi a ce Najeriya ce za ta taimaka wa yan ta’adda su yake ta, kuma ya kamata su san cewa idan sun kori Faransa sun kuma sake kawo wasu, to sun canja matsalar ne kawai, bai kamata su kawo wasu ba, duk wanda ya zo maka da farko zai zo a matsayin aboki ne, ko lokacin da suka kawo Faransa mun ba su wannan shawarar, amma basu ɗauka ba’’

    Ya ce Najeriya ba ta da niyyar nesanta kanta da maƙwabciyar ta ta, domin kasashen biyu da al’umominsu yan uwan juna ne, don haka kamata ya yi su hada kai su yi aiki tare, don ci gaban al’umominsu.

    A baya bayan nan ma sai da ministan harkokin wajen Nijar ɗin ya gayyaci jami’a mai kula da harkokin diflomasiyya a ofishin jakadancin Najeriya da ke ƙasar, don ta je ta yi bayani kan zargin da suke yi wa Najeriyar na hada kai da wasu kasashen Turai wajen shirya mata manaƙisa.

    Ministan ya yi zargi cewa, duk da irin na-mijin ƙoƙarin da Nijar ke ta yi na ganin ta kyautata dangantaka da daɗaɗɗiyar aminiya ko ma abokiyar tagwaitakar ta ta, watau Najeriya, amma ƙasar bata hakura ba, inda take ci gaba da haɗa kai da wasu manyan ƙasashen duniya da jami’an tsohuwar gwamnatin Bazoum da ke zaman mafaka a Najeryar ake ci gaba da kitsa yadda za a jefa ƙasar cikin hargitsi.

    Zarge zargen da shugaban Nijar ya yi wa Najeriya

    Shugaban na mulkin sojin Nijar ya ce daga bayanan da suka samu a daɗewa sun fahimci cewa na shirin kafa sansanin Lakurawa a wani daji da ke jihohin Sokoto da Zamfara da kuma Kebbi.

    ‘’Wasu manyan ‘yanta’adda da muka kama, sun shaida mana cewa a ranar 4 ga watan Maris ɗin shekarar 2024, Faransa ta ƙulla wata yarjejeniya da mayaƙan ISWAP, kuma shugabannin Najeriya na sane da ita, cewa za a mayar da dajin Gaba da ke jihohin Sokoto da Zamfara da Kebbi a Najeriya sansanin horas da mayaƙan Lakurawa’’, in ji shugaban na Nijar.

    Janar Tchiani ya yi zargin cewa an tanadin sansanin ne domin horas da mayaƙan Lakura don su watsu a jihohin Sokoto da Zamfara da kuma jihar Kebbi da kuma jamhuriyar Nijar.

    Shugaban na Nijar ya ce duk da iƙirarin mayaƙan da suka kama suka na cewa jagororin Najeriya na sane, ba su yarda da maganar ‘yan bindigar ba.

    Haka ma shugaban na Nijar ya zargi mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu da masaniya game da wannan batu.

    Yayin zargin cewa an ƙuduri aniyar horas da Lakurawan ne domin su kawo tarnaƙi ga aikin bututun man ƙasar da ka shimfiɗa zuwa Jamhuriyar Benin mai makwabtaka.

    Janar Tchiani ya zargi ƙasashe makwabtan Nijar da bai wa Faransa damar kafa sansanoni a ƙasashen domin horas da ‘yanta’adda da niyyar yaƙar Nijar.

    A baya-bayan nan dai dangantaka tsakanin Najeriya da Nijar na ci gaba da yin tsami, ko a makon da ya gabata ma gwamnatin mulkin sojin Nijar ɗin ta zargi Najeriya da shirya mata maƙarƙashiya, kodayake gwamnatin Najeriya ta musanta zargin.

    BBC HAUSA

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

    Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram WhatsApp

    Related Posts

    San Makwabciyarka Ta Hade Hannu da Majalisar Malamai

    July 24, 2025

    Gwamnatin Kano Ta Raba Takin Zamani Ga Manoma a Gwarzo

    July 22, 2025

    Halin Da Gwamnan Katsina Ke Ciki Bayan Hatsarin Mota

    July 21, 2025

    Kwamitin Gasar Karatun Alkur’ani Ya Koka da Zargin Almundahana

    July 21, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Editors Picks

    Kano Transport Commissioner Pulls Out as Surety in Drug Case

    July 26, 2025

    Renewed Hope Estate Kano Set for Tinubu’s Commissioning

    July 25, 2025

    Civil Society Group Warns Jigawa Against Short-Term Spending

    July 25, 2025

    Kano Advances Climate-Resilient Edu With FCDO/UNICEF Support

    July 25, 2025
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    Hajaj Albait 2
    © 2025 PARADIGM NEWS
    • Home
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.