Close Menu
PARADIGM NEWS
    Facebook X (Twitter) Instagram
    • Home
    • Privacy Policy
    Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
    PARADIGM NEWS
    • Home
    • Features

      I’ll dress elegantly for a week, lady vows as Kano women storm markets

      March 29, 2025

      Dr. Abdullahi Umar Ganduje’s Legacy of Progress and Excellence

      December 25, 2024

      The rise and fall of Faruk Lawan: A lesson in power and intrigues

      December 17, 2024

      Will The Axing of Zakirai Make Education Great In Kano

      December 17, 2024

      Harmattan Brings Boom to Tea, Noodle, Bean Cake Sellers in Kano

      December 15, 2024
    • News
      1. Local
      2. National
      3. International
      4. View All

      Fire Guts 45 Houses, 35 Silos in Batakashi Village Jigawa

      April 13, 2025

      Fake Charity Organization Allegedly Dupes Kano Residents

      April 6, 2025

      Chidari Urges Constituents to Uphold Islamic Values

      March 30, 2025

      Kano Lawmaker Provides Ramadan Support to Constituents

      March 16, 2025

      Nigeria Takes Bold Step Towards Eradicating Violence Against Children

      May 9, 2025

      Nigerian Delegation Heads to Vatican for Pope Francis’ Funeral

      April 25, 2025

      Inaugural Flight a Testament to FG, States Partnership – Minister

      April 23, 2025

      Akwa Ibom Gov Flags Off Section 3B of Lagos-Calabar Highway

      April 18, 2025

      Renowned Philanthropist Mrs. Maryam Imoke Yanah Recieves Warrior of Hope Award

      April 27, 2025

      Minister Woos French Investors with Nigeria’s Economic Reforms

      April 11, 2025

      Nigeria, Saudi Arabia Strengthen Anti-Drug Efforts

      April 9, 2025

      Info Minister Leads Delegation to US Broadcasters Conference

      April 7, 2025

      Kano Govt Disburses N600m Compensation to Erosion Victims

      May 9, 2025

      Kano Govt Bans Live Political Programs to Promote Peace

      May 8, 2025

      Governor Namadi Approves Minor Cabinet Reshuffle

      May 6, 2025

      When Stars Align: President Tinubu’s Visit to Katsina

      May 6, 2025
    • Politics

      Kwankwasiyya Ideology Dead In Kano Says Minister Ata

      May 7, 2025

      Just In: PDP Loses Another Governor: Delta’s Oborevwori Joins APC

      April 23, 2025

      Ganduje Inaugurates APC France, Drums support for Tinubu

      April 21, 2025

      No Vacancy For Number One Seat- Jigawa Sen Tells Contenders

      April 15, 2025

      Nigerians Abroad Back Seyi Tinubu for Lagos State Governor

      April 14, 2025
    • Conflict

      Kadpoly Retiree faults Committee, Demolition Of Property

      March 27, 2025

      President Tinubu Declares State of Emergency in Rivers State

      March 18, 2025

      El-Rufai Defends Najaatu Muhammad Against Ribadus Denials

      February 5, 2025

      Tinubu’s Corruption Saga: Najaatu-Ribadu Feud Takes Center Stage

      February 5, 2025

      Kano Inaugurates Committee to Investigate Rimin Zakara Dispute

      February 3, 2025
    • More
      • Analysis
      • Business
      • Crime
      • Cultural events
      • Economy
      • Education
      • Editorial
      • Entertainment
      • Environment
      • Fashion
      • Health
      • Lifestyle
      • Personality profile
      • Science
      • Sports
      • Technology
    • Hausa

      Murtala Sule Garo ya taya Alummar Musulmi Murnar Bikin Sallah

      March 31, 2025

      Gwamnatin Kano zata Sabuntawa Ma’aikatan Shara Kayan Aiki

      March 18, 2025

      Alummar Gwarzo Sun Yi Fitar Dango Don Tarbar Sabon Hakimin Su

      March 17, 2025

      Gidauniyar Dangote Ta Kaddamar Da Rabon Abinci Na Biliyan 16

      March 15, 2025

      KH Gwarzo Ta Kafa Kwamitin Rijiyoyin Burtsatsai Da na Kudin Shiga

      March 12, 2025
    Subscribe
    PARADIGM NEWS
    Hausa

    Murar Tsuntsaye: An Bukaci Alummar Kano su Kwantar da Hankalinsu

    EditorBy EditorJanuary 15, 2025Updated:January 15, 2025No Comments3 Mins Read
    Facebook Twitter Telegram WhatsApp
    IMG 20250114 WA0157

    Yayin da fargabar samun ɓarkewar annobar murar tsuntsaye a Kano ke ci gaba, gwamnatin jihar ta buƙaci al’umma da su kwantar da hankalinsu tare da kai rahoton duk wani zargi da ake da shi game da cutar ga hukumomin da abin ya shafa.

    No Cause for Alarm: Kano Government Addresses Bird Flu Rumors

    Raɗe-raɗin ɓullar annobar ya bayyana ne sakamakon wani rahoton da aka samu a watan Disamba na 2024 cewa wani matashi ɗan ƙaramar hukumar Gwale ya sayo agwagwa a kasuwar Janguza da ke ƙaramar hukumar Tofa ya haɗa ta da kajin da yake kiwo.

    Ad 4

    Nigeria’s Livestock Industry Attracts International Attention-Jega

    Daga baya sai ya lura kajin sun fara nuna alamun matsalar numfashi da har ta kai 35 cikin 50 sun mutu. Hakan ya sa ya kai wasu daga cikin waɗanda suka mutu asibitin dabbobi na Gwale domin yin bincike, inda a makon farko na watan Janairun 2025 sakamakon binciken ya nuna murar tsuntsaye ce ta yi sanadin mutuwar tasu.

    Samun sakamakon binciken ke da wuya, sai ma’aikatar noma ta je ta kulle wurin da mutumin ke yin kiwon tare da kashe ragowar kajin da yi wa wurin baki ɗaya feshin magani. Haka kuma, ma’aikatar ta yi irin wannan feshin a wurin da ake sayar da kaji a kasuwar Janguza tare da wayar wa masu sanaar kai game da illar murar tsuntsaye.

    Ad 3

    Kano Revitalizes Job Creation through Livestock Training Institutes

    Da tsokaci game da haka, a yau, Kwamishinan Lafiya, Dakta Abubakar Labaran Yusuf, a cikin wata sanarwar manema labarai daga sashin hulɗa da jama’a na ma’aikatar, ya buƙaci jama’ar jihar nan da su kwantar da hankalinsu saboda lamarin bai kai a kira shi ɓarkewar annoba ba.

    Kwamishinan ya ce ma’aikatar lafiya na tsaye sosai a kan al’amarin, tana da ɗaukar dukkan matakan da suka dace na tunkarar matsalar domin daƙile tasirinta kafin ta zama barazana.

    L-PRES Organizes Workshop On Improving Livestock Production

    Dakta Labaran ya ce kasancewar cutar murar tsuntsaye na harbar mutum tare da haddasa illa ga jiki ya sanya ya kira taro da kwamitocin Kar-ta-Kwana da na Lafiya Guda Ɗaya (Emergency Preparedness Response da One Health) da ke da wakilcin ma’aikatun noma, muhalli da albarkatun ruwa da kuma ƙungiyoyin ci-gaba domin a tattauna tare da tsara hanyoyin da za a tunkari al’amarin.

    Ya ce, “Wannan shi muke yi a halin yanzu. Za a rinƙa yin taro da masu ruwa da tsaki a kowane mako. Za a rinƙa sanar da al’umma a kai a kai halin da ake ci game da cutar.

    Nigeria’s Livestock Industry Attracts International Attention-Jega

    “Za a ƙarfafa sa ido a kowace ƙaramar hukuma, musamman tsakanin masu kiwon kaji da sauran tsuntsaye, sannan za a rinƙa bai wa waɗannan kwamitoci rahoto a kowace rana tare da sanar da Gwamna Abba Kabir Yusuf halin da ake ciki.”

    Kwamishinan ya ce alamomin cutar sun haɗa da zazzaɓi, fitar da majina, jan-ido da sauransu, inda ya buƙaci al’umma musamman masu kiwon kaji da su zama jami’an sa ido na farko saboda su kare ababen da suke kiwo da dukiyoyinsu, tare da kai rahoton duk wani yanayi da ke hana kajin walwala ga hukumomin da suka dace domin ɗaukar mataki a kan lokaci.

    Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram WhatsApp

    Related Posts

    Murtala Sule Garo ya taya Alummar Musulmi Murnar Bikin Sallah

    March 31, 2025

    Gwamnatin Kano zata Sabuntawa Ma’aikatan Shara Kayan Aiki

    March 18, 2025

    Alummar Gwarzo Sun Yi Fitar Dango Don Tarbar Sabon Hakimin Su

    March 17, 2025

    Gidauniyar Dangote Ta Kaddamar Da Rabon Abinci Na Biliyan 16

    March 15, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Editors Picks

    Nigeria Pushes Forward with Crude Sales in Naira Initiative

    May 9, 2025

    Nigeria Takes Bold Step Towards Eradicating Violence Against Children

    May 9, 2025

    KNSG to Showcase Plans at 2025 Nigeria Education Forum Summit

    May 9, 2025

    World Bank Delegation Visits Kano for ACReSAL Project Review

    May 9, 2025
    Hajaj Albait 2
    © 2025 PARADIGM NEWS
    • Home
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.