Close Menu
PARADIGM NEWS
    Facebook X (Twitter) Instagram
    • Home
    • Privacy Policy
    Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
    PARADIGM NEWS
    • Home
    • Features

      I’ll dress elegantly for a week, lady vows as Kano women storm markets

      March 29, 2025

      Dr. Abdullahi Umar Ganduje’s Legacy of Progress and Excellence

      December 25, 2024

      The rise and fall of Faruk Lawan: A lesson in power and intrigues

      December 17, 2024

      Will The Axing of Zakirai Make Education Great In Kano

      December 17, 2024

      Harmattan Brings Boom to Tea, Noodle, Bean Cake Sellers in Kano

      December 15, 2024
    • News
      1. Local
      2. National
      3. International
      4. View All

      NGO Empowers 50 GBV Survivors in Kano

      July 29, 2025

      KNSG Launches Safe Space for Women Battling Drug Addiction

      July 22, 2025

      Rescue Efforts End in Tragedy as Four Drown in Kano Waterway

      July 19, 2025

      Kano Assembly Denies Investigating ALGON Chair Hajiya Sa’adatu

      July 18, 2025

      NHIA, NSITF Unite to Bridge Gaps in Workers’ Welfare Schemes

      July 27, 2025

      Justice and Dignity at Heart of Nigeria’s Correctional Reforms- Minister

      July 27, 2025

      Renewed Hope Estate Kano Set for Tinubu’s Commissioning

      July 25, 2025

      Empower Youth to Drive Natl Development — NPC Tells Nigerians

      July 25, 2025

      Trump to Withdraw U.S. from UNESCO Again, Slams “Woke”

      July 29, 2025

      UN Summit: Africa Calls for Urgent Action on Global Food Crisis

      July 29, 2025

      Tinubu’s Green Diplomacy in Action as Nigeria Donates Cashew to Ethiopia

      July 28, 2025

      Just in: Saudi Arabia’s Sleeping Prince Dies After 19 Years in Coma

      July 20, 2025

      UNICEF Appoints Wafaa Saeed as New Country Representative in Nigeria

      July 29, 2025

      Jigawa State Disburses Over ₦1.5 Billion to 569 Retirees

      July 28, 2025

      KNHA Recommends Revocation of 5km Gabasawa Road Project

      July 28, 2025

      Minister Assures Swift Evacuation of Nigerians Abandoned in CAR

      July 27, 2025
    • Politics

      Just in : Atiku Quits PDP, Blames Party’s New Direction

      July 16, 2025

      Sule Lamido Backs Opposition Coalition Under ADC

      July 15, 2025

      Ringim Blames Sule Lamido, Not Wike, for PDP Crisis

      July 13, 2025

      Commissioner Waiya Endorses Women’s Political Representation

      July 7, 2025

      Gauta Club Gets 14 New Patrons as Waiya Champions Inclusive Politics

      July 5, 2025
    • Conflict

      Kadpoly Retiree faults Committee, Demolition Of Property

      March 27, 2025

      President Tinubu Declares State of Emergency in Rivers State

      March 18, 2025

      El-Rufai Defends Najaatu Muhammad Against Ribadus Denials

      February 5, 2025

      Tinubu’s Corruption Saga: Najaatu-Ribadu Feud Takes Center Stage

      February 5, 2025

      Kano Inaugurates Committee to Investigate Rimin Zakara Dispute

      February 3, 2025
    • More
      • Analysis
      • Business
      • Crime
      • Cultural events
      • Economy
      • Education
      • Editorial
      • Entertainment
      • Environment
      • Fashion
      • Health
      • Lifestyle
      • Personality profile
      • Science
      • Sports
      • Technology
    • Hausa

      Biza don Haihuwa:Amurka Ta Sanya Sabon Sharadi Ga Yan Najeriya

      July 29, 2025

      Likitoci a Legas Za Su Fara Yajin Aiki na Kwana Uku

      July 28, 2025

      PDP Ta Bukaci Fayose Ya Fice Daga Cikin Jam’iyyar

      July 28, 2025

      NYSC Ta Sha Kaye a Kotu Kan Haramta Siket Ga ‘Yan Mata

      July 28, 2025

      Labari Cikin Hotuna:Aisha Buhari ta Koma KD Domin yin Takaba

      July 28, 2025
    Subscribe
    PARADIGM NEWS
    Home » Mun Samu Kasuwancin Magunguna na Kano a Rikice -Kwamishina
    Hausa

    Mun Samu Kasuwancin Magunguna na Kano a Rikice -Kwamishina

    EditorBy EditorJanuary 23, 2025Updated:January 23, 2025No Comments4 Mins Read
    Facebook Twitter Telegram WhatsApp
    IMG 20250123 WA0096

    An bayyana cewa an samu kasuwancin magunguna na jihar Kano, bayan ƙarewar shekaru takwas na zangon mulki na biyu na Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, a cikin yanayi mara daɗi.

    Commissioner for Health Vows to Revamp Pharmaceutical Industry

    Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Abubakar Labaran Yusuf, ne ya bayyana haka yayin da yake karɓar shugabannin Кungiyar Masu Haɗa Magunguna da Sarrafa su ta Najeriya, reshen jihar Kano, da suka ziyarci shi a ofishinsa.

    Ad 4

    Ya koka da cewa sun samu kasuwar magani, musamman Hukumar Samar da Magunguna da Kayan Asibiti (DMCSA), hukuma ɗaya tilo da gwamnati ta amince ta samar wa asibitoci magunguna masu inganci da sauƙi, a durƙushe tana buƙatar ɗauki.

    Kwamishinan Lafiya Ya Yabawa K/H Uku Akan Rigakafin Shan Inna

    Dakta Labaran ya yi farin ciki da samun dunƙulalliyar kasuwar hada-hadar magunguna a Ɗangwauro kasancewar abubuwa sun fara dawowa daidai, ya ƙara da cewa abin da kawai ya rage shi ne tilasta amfani da kasuwar yadda ya kamata domin a tsaftace kasuwancin magunguna a jihar.

    Ad 3

    Kwamishinan ya ce sirrin da ke tattare da samun nasarar ayyukan samar da magunguna a Kano ta biyo bayan neman shawarar ƙwararru kan harkokin magunguna da yake yi game da duk wani abu da ya shafi harkar kafin ya tura wa Gwamna Abba Kabir Yusuf.

    K/H Garun Malam Ta Umarci ‘Yan Kasuwar Kwanar Gafan Da Su Tashi Cikin Kwanaki 7

    Ash Noor

    Ya bayyana cewa, gwamnatin Alhaji Abba Kabir Yusuf tana yin ayyukan da take yi ne domin al’umma, yana mai shawartar masu kasuwancin magani da su yi taka-tsantsan da jin tsoron Allah yayin da suke gudanar da ayyukansu, domin za a iya sake canja tare da sarrafa maganin da wa’adinsa ya ƙare a sake mayar da su kasuwa, yana mai yarda da cewa mutum mai tsoron Allah bai zai yi irin wannan ƙazamin kasuwancin ba.

    Dakta Labaran ya ce ya yi farin ciki sosai da ɗaukar nauyin ɗalibai zuwa ƙasar Indiya su yi karatun haɗa magunguna da sarrafa su a lokacin da yake kwamishina a tsakanin shekarar 2011 da 2015, ya ce a lokacin ‘yan Kano masu rajista a wannan ilimin 51 ne kawai, wanda hakan ya sa Gwamna Kwankwaso ya umarce shi ya tantance mutum 100 aka tura su Indiya, da mafi yawansu yanzu haka suna hidimta wa Kano.

    Da yake jawabi tun da fari, Shugaban Кungiyar, Famasis Mustafa Umar ya ce sun zo ma’aikatar ne domin su nuna goyon bayansu ga ƙoƙarin kwamishinan na kawo sauyi a sashin lafiya na jihar nan.

    Ya nuna farin cikinsa da cewa dawowar kwamishina ta zo a lokacin da ya dace saboda masu ilimin haɗa magunguna da sarrafa su na jihar Kano suna cikin damuwa mai tsanani game da makomar DMCSA, amma yanzu sun samu nutsuwa saboda abubuwa sun fara dawowa daidai da ta kai yanzu ake samun magani kashi 96 cikin 100 a asibitoci idan an kwatanta da baya da ake samun kaso 30 kawai.

    Shugaban ya gode wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa naɗa ɗaya daga cikinsu, Famasis Aminu Bashir a matsayin Babban Sakatare, wanda shi ne irinsa na farko a tarihin jihar Kano, yana mai tabbatar da cewa babban sakataren zai yi aiki tuƙuru wajen ci gaban aikin gwamnati duba da ƙwazo da jajircewarsa a aiki.

    Daga nan sai ya sanar da kwamishinan cewa a watan Nuwamba, na wannan shekarar, jihar Kano za ta karɓi baƙuncin taron Кungiyar Masu Samar da Magunguna da Sarrafa su da ake sa ran ‘ya’yan ƙungiyar dubu uku zuwa dubu biyar za su ziyarci Kano, inda ya nemi gudummawar gwamnati.

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

     

    Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram WhatsApp

    Related Posts

    Biza don Haihuwa:Amurka Ta Sanya Sabon Sharadi Ga Yan Najeriya

    July 29, 2025

    Likitoci a Legas Za Su Fara Yajin Aiki na Kwana Uku

    July 28, 2025

    PDP Ta Bukaci Fayose Ya Fice Daga Cikin Jam’iyyar

    July 28, 2025

    NYSC Ta Sha Kaye a Kotu Kan Haramta Siket Ga ‘Yan Mata

    July 28, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Editors Picks

    UNICEF Urges Kano to Extend Maternity Leave, Invest More in MNCH

    July 29, 2025

    2025 MNCHW: Kano Distributes 6,000 Delivery Packs, 500 C/S Kits

    July 29, 2025

    UNICEF Appoints Wafaa Saeed as New Country Representative in Nigeria

    July 29, 2025

    Kano Unveils Climate Change Policy, Targets 5M Tree Planting

    July 29, 2025
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    Hajaj Albait 2
    © 2025 PARADIGM NEWS
    • Home
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.