Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta kama wata mata mai shekaru 25 mai suna Nafisa Usman bisa zargin safarar harsasai tsakanin jihohi, inda aka same ta da sabbin harsasai guda 200.
Rahotanni sun ce an cafke ta ne a wata babbar tashar mota a Kano, bayan ta ɓoye harsasan cikin buhunan garri da shinkafa, tana ƙoƙarin jigilar su daga Nasarawa zuwa Kankara a jihar Katsina.
DSS ta bayyana cewa an kama ta ne bayan samun sahihan bayanan sirri, kuma ta fito daga ƙauyen Zango da ke ƙaramar hukumar Kankara.
A cewar hukumar, wacce ake zargin ta amsa cewa ana kawo mata harsasan daga Lafia, sannan a rarraba su zuwa hannun ‘yanbindiga a dajin Kankara, ciki har da wani da ake kira Mallam Haruna.
Ta kuma ce ta shafe kusan watanni biyu tana wannan sana’a, tare da yin mu’amala da ta kai kusan naira miliyan 5.
Hukumar DSS ta ce za ta gurfanar da wacce ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

