An shiga cikin fargaba a birnin Sakkwato ranar Juma’a bayan da wani matashi ya daɓa wa wani malamin addinin Musulunci, Sheikh Musa Lukwa, jim kaɗan bayan ya jagoranci sallar Juma’a a masallacinsa da ke unguwar Mabera a birnin Sokoto.
Rahotanni sun ce matashin na cikin masu ibadar da suka halarci sallar, inda ake zargin ya caka masa wuƙa sau biyu a wuya, lamarin da ya nan da nan aka garzaya da shi asibiti.
Read also: MRA Organizes Workshops On Laws Affecting Media In Nigeria
Read also: Death of Iran’s Supreme Leader Khamenei Sparks Regional Crisis
Wani bidiyo da malamin ya wallafa a shafinsa na Facebook, jim kaɗan bayan sallamarsa daga asibitin ya nuna wuyansa ɗaure da bandeji, inda yake kiran magoya bayansa su kwantar da hankali.
Read also: Kebbi Police Arrest Two Suspects for Sexually Assaulting Minors
”Jama’a kowa ya kwantar da hankalisa, ina cikin ƙoshin lafiya, babu wata matsala, lafiyar ƙalau nake ban jin komai ga jikina, Allah ya bani kariya”, kamar yadda ya bayyana a cikin bidiyon mai tsawo sakan 32.
BBC HAUSA

