Lauya kuma mai fafutukar kare hakkin jama’a, Barista Abba Hikima Fagge, ya miƙa ƙorafi a hukumance ga Sufeto Janar na ‘Yan Sandan Najeriya, inda ya buƙaci a gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa kan zargin da ake yi na kisan Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata.
A cikin takardar ƙorafin da aka rubuta ranar 8 ga Mayu, 2026, lauyan ya bayyana cewa wani mutum mai suna Muhammad Musa Kamarawa ya yi ikirarin cewa ya kasance shaida kan yadda wasu jami’an ‘yan sanda suka kashe Dadiyata.
Takardar ta kuma nuna cewa zargin ya ambaci sunayen wasu jami’an ‘yan sanda biyu, lamarin da ya sa aka buƙaci a gaggauta gudanar da bincike domin tabbatar da gaskiya da kuma kawar da shakku.
Barista Fagge ya jaddada cewa idan zargin ya tabbata ƙarya ne, binciken zai wanke sunayen waɗanda ake zargi. Sai dai idan ya tabbata akwai gaskiya a cikinsa, dole ne a tabbatar da an yi adalci ba tare da la’akari da matsayi ko iko ba.
Ya kuma bayyana cewa batun batan Dadiyata tun daga shekarar 2019 ya dade yana haifar da damuwa da tambayoyi a tsakanin jama’a, don haka sabon zargin ya ƙara buƙatar a ɗauki matakin gaggawa.
A ƙarshe, ya roƙi ofishin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda da ya kafa kwamitin bincike mai zaman kansa domin zurfafa bincike tare da bayyana sakamakon ga jama’a domin tabbatar da gaskiya da adalci.
Lamarin na ci gaba da jan hankalin jama’a, inda ake ci gaba da kira ga hukumomi da su ɗauki matakin da ya dace domin warware shari’ar da ke ɗauke da manyan tambayoyi tun shekaru.

