Jagoran jam’iyyar NNPP na ƙasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayar da umarnin bai wa ’ya’yan wasu ’yan majalisar dokokin jihar Kano biyu da suka rasu tikitin takara domin fafatawa a zaɓen cike gurbi na kujerun majalisar dokokin jihar.
Rahotanni sun nuna cewa ’ya’yan ’yan majalisar da suka rasu sun zama ’yan takarar majalisar dokokin jihar Kano a ƙarƙashin tutar jam’iyyar NNPP.
A farkon makon da muke ciki ne, ƴan majalisar jiha, Hon. Aminu Sa’adu Ungoggo da Sarki Aliyu Daneji suka rasu a Rana daya, lamarin da ya jefa al’ummar jihar cikin alhini.
Mai taimaka wa Sanata Kwankwaso ta fannin kafafen yaɗa labarai, Saifullahi Hassan ne ya bayyana hakan cikin wani sako da ya wallafa a shafin Facebook a yammacin ranar Asabar.
Majiyoyi daga bangaren iyalan ’yan majalisar da suka rasu, tare da wasu jagororin jam’iyyar NNPP a ƙaramar hukumar Birnin Kano, suma sun tabbatar wa da Daily Nigerian Hausa wannan mataki.
Daily Nigerian Hausa

