Safiyanu Dantala Jobawa
Maigirma shugaban karamar hukumar Garun mallam Hon Barr Aminu Salisu Kadawa ya kai ziyar taya murnar biki kirsimeti ga mabiya addinin Kirista dake Yantomo.
Read also: Kano MoPB, KanSLAM Lead Dialogue on MNCH,FP Financing
Kwamishina ta Taya Gwamnan Kano Murnar Sabuwar Shekara
Ya yi kira gare su da su cigaba da yiwa kasa addu’a don kara samun zaman lafiya a tsakanin mabiya addinai daban-daban.
A karshe ya mika goron bikin kirsimeti na naira dubu dari biyu nan take.
Mabiyan sun nuna murnarsu ga yadda akwai kyakkyar alaka dake tsakaninu da mabiya addinin musulunci. Sun kuma mika godiya da irin nuna musu halaci da aka yi tare da godiya da mika musu goran barka da kirsimeti.
Kano a Shirye Take ta Yaki Kwalara da Sauran Cututtuka – KNCDC
Read also: Kano State Government Opposes Proposed Tax Reform Bill
A cikin tawagar maigirma shugaban karamar hukumar akwai mataimakinsa Hon Tasiu S Kwiwa da kakakin majalisar kansuloli Hon Aliyu Abdulhamid Dakasoye da kansulolin yankin da limamai da sauransu
Read also: Kano State Gov. Correspondents’ Chapel Meet to Resolve Impasse

