Ministan Wutar Lantarki, Joseph Tegbe, ya bayyana cewa wasu masu amfani da wutar lantarki a Nijeriya sun roƙe shi da a rage yawan wutar da ake samar musu, sakamakon ingantuwar samar da wutar lantarki a ƙasar.
Ministan ya ce wasu daga cikin masu amfani da wutar sun bayyana cewa yawan wutar da suke samu ya sa “firijinsu na daskarewa sosai”.
Read also: Wife Of Jigawa Governor Pledges More Support For Girls Education
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Tegbe ya bayyana hakan ne a ranar Laraba, yayin ƙaddamar da aikin samar da hasken lantarki mai amfani da hasken rana, mai ƙarfin megawatt uku, a Jami’ar Abuja.
Read also: NAWOJ Kano Mourns Passing of Business Icon Aminu Dantata
Ya ce al’ummar Nijeriya na ci gaba da cin gajiyar sauye-sauyen da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa a fannin wutar lantarki.
Tegbe ya bayyana ci gaban da aka samu a fannin a matsayin wani mataki da ke nuna cewa gyare-gyaren da ake yi a ɓangaren samarwa da rarraba wutar lantarki na fara haifar da sakamako.
Read also: Barista Abba Hikima Ya Shigar da Korafi Kan Zargin Kisan Dadiyata
Ya ƙara da cewa ƙarin samar da wutar lantarki zai taimaka wajen bunƙasa harkokin kasuwanci, ilimi da sauran ayyukan ci gaba a ƙasar.
Daily Trust

