Wata kotun yanki da ke zama a Centre-Igboro a Ilorin, jihar Kwara, ta raba auren da ke tsakanin Toyin Ajibola da matarsa, Bashirat Mohammed, sakamakon talauci da mijin ke fama da shi.
Alkalin kotun, Hammad Ajumonbi, ne ya yanke hukuncin bayan Bashirat ta garzaya kotu tana neman a raba aurensu, inda ta koka kan tsananin matsin rayuwa da kuma abin da ta bayyana a matsayin rashin ɗaukar nauyi daga mijinta.
Read also: Kano Citizens advocates for enhanced enrollment in BHCPF
“Ina roƙon kotu ta raba auren nan domin in samu nutsuwar zuciya,” in ji Bashirat a gaban kotu.
Sai dai Ajibola ya shaida wa kotu cewa har yanzu yana son ci gaba da aurensu duk da matsalolin kuɗin da yake fuskanta.
Read also: NUGA:FG Commits ₦1 Billion to Upgrade UNIJOS Sports Arena
A hukuncinsa, Ajumonbi ya ce duk da cewa Ajibola ya nuna sha’awar ci gaba da aure, bai dace a tilasta wa mace ta ci gaba da zama a auren da ba ta so ba.
Alkalin ya ce Bashirat na buƙatar ci gaba da rayuwarta domin kada ta shiga cikin mawuyacin hali, don haka ya bayar da umarnin raba auren.
Read also: Jami’ar Bayero ta Kano Za Ta Gina Gidajen Ma’aikata 500
Har ila yau, kotun ta umarci Bashirat da ta yi iddah na tsawon watanni uku kafin ta sake yin wani auren.
Daily Nigerian Hausa

