Jiga-jigan siyasar jihar Rivers masu biyayya ga Ministan Abuja, Nyesom Wike, sun mamaye tikitin takarar kujerun majalisar wakilai ta jam’iyyar APC a zaben fidda gwani da aka gudanar a jihar.
Daga cikin wadanda suka samu tikitin akwai Kakakin Majalisar Dokokin Rivers, Martin Amaewhule, da dan majalisar wakilai, Dum Dekor.
Rahoton ya nuna cewa magoya bayan Gwamna Siminalayi Fubara ba su samu gagarumar nasara ba duk da sauyawar gwamnan daga PDP zuwa APC.
Jam’iyyar APC ta ce an gudanar da zaben cikin lumana a dukkan mazabu 13 na tarayya ba tare da tashin hankali ba, lamarin da shugabannin jam’iyyar suka yabawa mambobinta.
Shugaban kwamitin gudanar da zaben fidda gwanin APC a jihar, Wahab Owokoniran, ya bayyana cewa babu wata hayaniya ko rikici da aka samu yayin gudanar da zaben, yana mai cewa hakan ya saba da yadda ake kallon siyasar Rivers a matsayin mai cike da tashin hankali.
Daga cikin wadanda suka samu tikitin akwai Solomon Bob, Victor Obuzor, Isobo Jack, Frederick Apiafi, Cyril Hart, Felix Nwaeke, Linda Stewart da sauran ‘yan takara daga mazabu daban-daban na jihar.
Sakataren yada labaran APC a Rivers, Chibuike Ikenga, ya ce sakamakon zaben ya fito ne daga zabin da mambobin jam’iyyar suka yi cikin gaskiya da adalci.
Daily Nigerian Hausa

