Ƙungiyar Dattawa da shugabannin Jihar Rivers, ta nuna damuwa kan sanarwar neman tsige Gwamna Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa, Farfesa Ngozi Ordu.
Shugaban riƙon ƙungiyar, Dr. Gabriel Toby, wanda tsohon mataimakin gwamnan jihar ne, ya soki wannan yunkuri a cikin wata sanarwa da aka fitar a Port Harcourt ranar Asabar.
Read also: APS, UNICEF Urge Early Antenatal Care to Reduce Maternal Deaths
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa ‘yanmajalisar dokokin jihar Rivers sun bayyana shirinsu na tsige Fubara bayan wani taron gaggawa da suka yi ranar Laraba.
Read also: Prof. Bukar Emerges Pioneer Chairman Borno Zakkat Commission
Mr Toby ya ja hankalin cewa tsigewa wani muhimmin tsari ne a kundin tsarin mulki, bai kamata a yi amfani da shi don biyan bukatun siyasa ko rikicin ɓangaranci ba.
Read also: Kano Pillars Dismal Performance: Where Government Got it Wrong
A cewarsa, dalilan da ‘yan majalisar suka bayar don yunkurin tsige gwamnan ba su da ƙarfi, ba su da inganci kuma babu wani uzurin da ya shafi muradun jama’a ko kuma da ya yi daidai da tanadin kundin tsarin mulki.
Daily Nigerian Hausa

