Close Menu
PARADIGM NEWS
    Facebook X (Twitter) Instagram
    PARADIGM NEWS
    • Home
    • About Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy
    • Features

      Diphtheria in Kano: How Zero-Dose, Late Treatment, Misinformation Are Fueling Persistent Outbreak

      August 29, 2026

      From Financial Struggles to Joy: How Kano’s Mass Wedding Changed 1,500 Lives

      August 8, 2026

      Water Scarcity Fuels Booming Water Vendor Business in Kano

      June 17, 2026

      Against All Odds: How Second Chance Education is Transforming the Lives of Married Girls in Northern Nigeria

      May 21, 2026

      How Kano’s Grassroots Communities Are Responding to eBR

      May 17, 2026
    • News
      1. Local
      2. National
      3. International
      4. View All

      Speaker Commissions Development Projects in Zaria

      September 20, 2026

      V-PeSDI Takes Disability Inclusion Campaign to 6 Kano LGAs

      September 15, 2026

      Support Nasir for 2nd Term, SRRBDA Boss Urges Kebbi Voters

      September 13, 2026

      NOA Seeks Zazzau Emirate Support to Fight Drug Abuse

      September 11, 2026

      No Nigerian Should Die in Government Custody-Tinubu

      September 19, 2026

      NEMA DG Inspects Contact Centre, Trigger Room in Abuja

      September 17, 2026

      NIMC Targets Grassroots Nigerians With Electronic Registration

      September 17, 2026

      FG Empowers Youths With AI, Fashion, Solar Skills

      September 15, 2026

      NASC Participates in India-Africa Seed Summit 2026

      September 17, 2026

      US Arrests Nigerian Woman Over Alleged Illegal Voting

      September 17, 2026

      IGAD Council Reviews Regional Peace, Security Challenges

      September 15, 2026

      Women’s Leadership Vital to Africa’s Peace, Stability-AU

      September 15, 2026

      KOMC Calls for Accuracy, Fairness in Election Reporting

      September 20, 2026

      RMAFC Reconstitutes Committee to Verify Disputed Oil, Gas Wells

      September 17, 2026

      HYPADEC, NOA Strengthen Public Awareness in Kogi

      September 17, 2026

      NERC Backs Continued Collaboration With Mainstream Energy

      September 16, 2026
    • Politics

      Kwankwasiyya Alleges Political Intimidation, Demands Probe

      September 16, 2026

      Minister Lists Economy, Education, Security Gains Under Tinubu

      September 11, 2026

      2027: Bishops Throw Weight Behind Tinubu, Call for National Unity

      September 10, 2026

      Babandede Rejects Defection Speculation, Declares Loyalty to APC

      September 9, 2026

      2027 Elections: Kano Govt Warns Against Hate Speech, Violence

      September 9, 2026
    • Conflict

      IPCR, GI-TOC Hold Strategic Roundtable on Crime–Conflict Nexus

      May 29, 2026

      Natasha Livestreams Faceoff With Immigration Over Passport Seizure

      November 4, 2025

      Kebbi Gov’t Threatens Legal Action Against Malami Over Defamation Claims

      September 19, 2025

      FG Calls for Conflict-Sensitive Climate Adaptation to Tackle Insecurity

      September 3, 2025

      Kadpoly Retiree faults Committee, Demolition Of Property

      March 27, 2025
    • Advertise With Us
    • More
      1. Analysis
      2. Business
      3. Crime
      4. Cultural events
      5. Economy
      6. Education
      7. Editorial
      8. Entertainment
      9. Environment
      10. Fashion
      11. Health
      12. Lifestyle
      13. Personality profile
      14. Science
      15. Sports
      16. Technology
      17. View All

      Ratko Mladić: The Butcher of Bosnia and the Shadow He Leaves Behind

      August 28, 2026

      Meet Ibrahim Garba, Spokesperson to Kano NDC Governorship Candidate

      July 26, 2026

      MK Tecnic Reinvents Digital Brand with Edu, Value-Driven Content

      July 24, 2026

      FreeTV Represents Nigeria’s Broadcasting Future, Not A Departure From DSO Vision

      May 14, 2026

      SMEDAN, EFCC Partner to Promote Made-in-Nigeria Products

      September 17, 2026

      Why Uber Is Leaving Nigeria After 12 Years of Operations

      September 3, 2026

      KIRS, SWAN Partner to Empower Women Accountants, Businesses

      August 18, 2026

      Nestlé Milo Empowers Kano Tea Sellers with Business Tools

      August 16, 2026

      Osun NSCDC Arrests Father, Son Over Stolen Power Cables

      September 14, 2026

      7-Year-Old Girl Allegedly Tortured by Mother in Anambra

      September 14, 2026

      Father Jailed After Threatening to Behead Son’s Teacher

      September 11, 2026

      Kano: Two Men Jailed Nine Years for Supplying Intoxicants to Children

      September 9, 2026

      Emir of Gwandu’s 21-Year Reign Marked by Peace, Dev-NUJ

      June 7, 2026

      Zazzau Emirate Set for Grand Turbaning as Ibrahim Jibril Becomes Sarkin Yaki

      March 30, 2026

      Argungu Fishing Festival Shows Nigeria’s Strength,Cultural Pride-Tinubu

      February 15, 2026

      Giant 59kg Fish Sparks Excitement as Tinubu Launches Argungu Festival

      February 14, 2026

      Lagos Joins Stakeholders to Drive Nigeria’s $100bn Creative Economy

      September 17, 2026

      Zazzau Emirate, Gates Foundation Forge Partnership on Economic Empower

      September 10, 2026

      Orange Economy: FG Backs NIPSS Plan to Unlock 48 Creative Sectors

      September 9, 2026

      Kano’s Crafts, Fashion, Film Will Drive Economic Growth-Gov Yusuf

      August 17, 2026

      Education Can Help Curb Rural-Urban Migration-Sumaila

      September 20, 2026

      SSANU Targets More Women in University Decision-Making

      September 19, 2026

      NWUK Trains Researchers on TETFund NRF Grant Writing

      September 18, 2026

      BUK Registrar Set for 2026 AfricanAGE Excellence Award

      September 18, 2026

      Another Grid Collapse, Another Missed Opportunity

      February 3, 2026

      Debunking Myths: Every Girl Deserves Education After Menarche

      August 16, 2025

      How External Forces Shape Electoral Outcomes

      May 8, 2025

      Media Narrative: Between Tinubu’s Birthday and the Lynching of Northerners in Uromi

      March 31, 2025

      SONTA Honours Varsity Don, Prof. Taofiq Nasir, With Lifetime Achievement Award

      August 22, 2026

      Kannywood Celebrities Face One-Year Suspension in Kano

      May 17, 2026

      Security Alerts Disrupt UROMI-16 Premiere in Northern Nigeria

      April 23, 2026

      Nigerian Actor Dumps ‘Papa Ajasco’ Persona, Unveils New Name

      March 22, 2026

      Environment Ministry Inspects AAAU for REA Solar Farm

      September 19, 2026

      Green Kaduna 2026: ABUTH Hosts Tree Planting Initiative

      September 18, 2026

      N-HYPPADEC, NCCC Explore Funding for Climate Resilience

      September 17, 2026

      CCAC Project Promotes Soot-Free Buses in Nigeria

      September 14, 2026

      Princess Diana Named Ultimate Female Style Icon

      September 5, 2026

      Kamfanin Louis Vuitton ya ƙirƙiri jakar dutse da ruwan zinari

      October 8, 2025

      Icon of Modern Fashion, Giorgio Armani, Dies at 91

      September 4, 2025

      Celebrities Designers Kicked Off Paris Couture Fashion Week

      April 16, 2024

      108 Donate Blood at Global Shapers Annual Drive in Kano

      September 19, 2026

      NAFDAC Confirms Methanol in Ondo Concoctions as Death Toll Hits 48

      September 19, 2026

      Kebbi Health College Joins JAMB E-Facility After Accreditation

      September 18, 2026

      Taraba Confirms Diphtheria Outbreak After One Death

      September 17, 2026

      Duchess Of Sussex Meghan Markel Launches New Lifestyle Brand

      April 18, 2024

      Who Is Dr. Lawan Ahmed Sani II? Meet the New Emir of Gumel

      September 7, 2026

      Sa’a Ibrahim: A Trailblazer in Nigerian Broadcasting, Media Leadership

      August 12, 2026

      I Was Left to Die as a Baby’-Dalung Shares Emotional Story Behind Activism

      July 17, 2026

      NUJ Politics: A Legacy of Service by Bello Mujtaba

      January 12, 2026

      KNSG Distributes 700 Fire Extinguishers to STSB Colleges

      September 20, 2026

      BUK VC Haruna Musa Honoured With NiBSA Award

      September 19, 2026

      NNRA Delegation Attends IAEA General Conference in Vienna

      September 16, 2026

      ABU Donates 45 Refurbished Microscopes to 8 Schools in Zaria

      August 15, 2026

      World Cup 2026: Yamal Rejects FIFA Choice, Names Best Player

      September 19, 2026

      JUST IN: Kano Sports Officials, Driver Escape Death

      September 14, 2026

      BUK Clinches Tug of War Gold at KASHIGA Staff Games

      September 14, 2026

      Sports Unites Nigerians, Projects Nigeria’s Image-Nestlé Milo

      September 6, 2026

      NDPC, NiDCOM Explore Joint Action on Data Privacy

      September 17, 2026

      NDPC Commissions New Headquarters in Abuja

      September 16, 2026

      FG Targets 32,000 Nigerians With Digital Skills Training

      September 15, 2026

      NNRA, EU Strengthen Nigeria’s Radioactive Waste Regulation

      September 8, 2026

      NAHCON Ta Karyata Zargin Karkatar da Kujeru 5,000

      September 20, 2026

      KNSG Distributes 700 Fire Extinguishers to STSB Colleges

      September 20, 2026

      Speaker Commissions Development Projects in Zaria

      September 20, 2026

      KOMC Calls for Accuracy, Fairness in Election Reporting

      September 20, 2026
    • Hausa

      NAHCON Ta Karyata Zargin Karkatar da Kujeru 5,000

      September 20, 2026

      Ƴan Nijeriya na roƙon a rage wutar lantarki saboda firijinsu na daskarewa’

      September 17, 2026

      Bidiyon Wanka da Mata: Hisbah Ta Kama Fitaccen Ɗan TikTok

      September 17, 2026

      An rufe shagon maganin gargajiya na Kashiful Aleel

      September 12, 2026

      Harin Wuƙa: An Sallami Sheikh Lukuwa Daga Asibiti

      September 12, 2026
    PARADIGM NEWS
    Home»Hausa»NAHCON Ta Karyata Zargin Karkatar da Kujeru 5,000
    Hausa

    NAHCON Ta Karyata Zargin Karkatar da Kujeru 5,000

    EditorBy EditorSeptember 20, 2026Updated:September 20, 2026No Comments8 Mins Read
    Facebook Twitter Telegram WhatsApp

    Hukumar da ke Shirya Aikin Hajji ta Kasa a Najeriya (NAHCON) ta bayyana cewa an ja hankalinta kan wani rahoto da gidan jaridar THISDAY ya wallafa mai taken” 2027 HAJJ: Masu shirya Aikin Hajji Masu Zaman Kansu Sun Bukaci bayani kan Karkatar da Kujerun Aikin Hajji 5,000,” baya ga wasu labarai da ke zama na karya da wasu tsirarun masu lasisin shirya aikin Hajji suke yadawa a dangane da kujerun aikin Hajjin na 2027.

    A cewar martanin ko sanarwar da Hukumar ta NAHCON ta fitar dauke da sa hannun Shafii Sani Mohammed babban jami’i mai kula da harkokin yada labarai da wallafa a hukumar ta NAHCON, yace duk da cewa masu ruwa da tsaki na bukatar ayi masu bayani kan abin da ya shafi harkokin aikin Hajji, yana da kyau a san muhimmanci na banbance gaskiya daga jita-jita dama lura da wasu abubuwan da ake yi bisa wata bukata ta kasuwanci.

    Read also: Daura Emir Confers Traditional Title On Hajiya Baraka Sani

    Sanarwar tace hukumar tana sane da yadda ake tsara wasu zarge-zarge marasa tushe kan batun na “Karkatar da Kujerun aikin Hajji” mai makon a bayyana wasu abubuwa da aka yi bisa kuskure, sai ake fitar da wasu zarge-zarge don kawar da hankali, daga batun gazawar masu shirya aikin Hajjin masu zaman kansu kan wasu sharuda masu tsauri da ake gindaya masu da wa’adi da ake basu da bin tsarin shigar da bayanai a tsarin fasahar zamani ta digital, sharudan da hukumar Aikin Hajji da Umrah ta kasar Saudiyya ta gindaya su saboda Hajjin da za a yi a 2027.

    Abin lura shine yadda aka rubuta rahoton ba tare da bayyana wanda ke zargin hukumar ba sai kawai aka kira su da sunan “Masu ta cewa kan abin da ya shafi masu shirya tafiye-tafiye da ke zaman kansu,” Ba a fayyacewa masu karatu shin su waye wadannan masu shirya tafiye-tafiye, shin masu ruwa da tsaki ne ko kuwa wadanda suka gaza samun damar yin wannan aiki ne, ko wadanda suke gasa da takwarorinsu ko kuwa wadanda damar da aka basu bata dace da bukatarsu ba ta kasuwanci. Rashin bayyana kai ya sanya masu karatu sun gaza gano sahihancinsu da dalilin yin haka ko manufarsu.

    Wani abun mai muhimmanci shine, duk da cewa wannan zargi abu ne da ke bukatar taka tsantsan, babu wata sheda da aka gabatar da ta nuna cewa ga wani abu da aka yi bisa kuskure.

    Isa Kaita College

    Babu inda aka nuna ba da wadannan kujeru 5,000 an sabawa dokar kasar Saudiyya ko sharudan hukumar NAHCON ko duk wani tsari da ya shafi yadda ake gudanar da aikin Hajji a Najeriya. Bayanan dai sun fi kama da zato ko wata bukata ta kasuwanci, an gaza gabatar da hujja da ta nuna an karya doka ko wasu ka’idoji .

    Tabbas, wannan rahoto ma ya nuna cewa hukumar ta NAHCON tayi bayani dalla-dalla kan yadda aka rarraba kujerun na aikin Hajji.Hukumar ta bayyana karara cewa kujerun da aka bawa Najeriya a Hajji 2027, su 50,000 ne,kuma kujeru 35,000 an ware domin jihohi da Babban Birnin Tarayyar Najeriya Abuja sai kuma kujeru 15,000 da aka bawa masu jigilar aikin Hajji da ke zaman kansu da suke da lasisi.

    Wadannan kujeru 15,000 an ware su ne ga masu shirya aikin hajjin da suke da lasisi kuma suke aiki karkashin kamfanoni (7) da aka aminta da su kamar yadda yake karkashin sharuda da aka gindaya a Najeriya da Kasa mai Tsarki ta Saudiyya.

    NAHCON ta kara fayyace bayani da cewa kamafanoni da za su yi aikin Hajji da Umrah a 2027 kamfanoni ne da aka san da su wadanda ke da rijistar hukumar Corporate Affairs Commission (CAC) da wasu hukumomi na gwamnati da ke sanya idanu, kuma sai sun bi sharudan da ake gindayawa, kuma hukumar ta NAHCON ta basu lasisi cewa ta amince su gudanar da aikin Hajji da Umrah a 2027.

    Duk da haka suna karkashin dokoki da tsari da ma iya fuskantar hukunci da ake iya yiwa duk mai gudanar da harkokinsa na jigila mai lasisi.

    Sanarwar har ila yau ta kara da cewa ko da wasu masu ruwa da tsakin sun aminta da bayanan na NAHCON, wani abu ne na daban; a bangare guda idan za a yi adalci dole a fara duba matsayin hukumar bisa cancanta, ba wai a rufe idanu ba da zarge-zarge da bata suna.

    “Magana ta gaskiya wanann cece-kucen ya fi kama da batu na kasuwanci, Harkokin aikin Hajji abune da ya shafi tattalin arziki inda za ka ga kamfanoni da dama suna fafutuka kan samun kujeru kayadaddu a tsakanin junansu.” A cewar sanarwar.

    Ta kara da cewa batu ne kawai na na me masu kamfanonin za su samu ba ma batun ba da kariya ga mahajjata ba.

    Read also: Data Sales Shift Online as Kano Vendors Battle Declining Patronage

    Hukumar ta NAHCON ta kara da jan hankali na al’umma cewa “kalubalen da ke gaban masu shirya jigilar shine tsarin Saudi Nusuk-Masar da ke tafiya da lokaci a tsarin fasahar zamani na digital. Mahukunta a kasar Saudiyya sun bayyana karara cewa hanyar dora bayanan mahajjata da yi masu rijista za a rufe ranar 26 ga Satumba,2026.” Tace umarnin na ranar karshe daga hukumar ta kasar Saudiiya ne ba NAHCON ba, don ita bata hurumi na kara ko da minta daya ne.

    A cewar sanarwar abin takaici maimakon mayar da hankali kan yin rijistar masu aniyar tafiya da sanya bayanan haihuwarsu da biyan kudade cikin lokacin da aka ka’idance, sai wasu daga cikin masu kamfanonin suka zabi bata lokacinsu wajen kirkirar labaran kanzon kurege da shirya labarai da za su boye matsalolin da suke da su wajen gudanar da ayyukansu.

    Hukumar tace ba za ta lamunta ba tana gani kudaden da al’umma suka tattara wajen ganin sun sauke farali daga Najeriya a wofuntar da su saboda masu shirya jigilar sun gaza yin abin da ya dace na bin ka’idoji da Saudiyya ta gindaya. “Walwalar mahajjata muhimmiya ce dole duk masu jigila da ke da lasisi, ana bukatar ganin sun cika sharuda na yin abin da ake bukata cikin lokacin da Saudiyya ta ayyana”. A cewar hukumar.

    NAHCON tace tana tattara bayanai na labaran karya da ake shiryawa da gangan don karkatar da hankali, a yaudari mahajjata da kokari sanya shakku ko karya gwiwa kan yadda hukumar ke gudanar da ayyukanta na tsarin aikin Hajji.

    “Duk masu shirya jigilar aikin Hajji da suka gaza sanya bayanan masu aniyar aikin Hajji wanda ke cikin sharadi na biyansu kudade kafin lokacin da Saudiyya za ta rufe damar da ta bayar, su za a kama da alhakin rashin cika sharudan.”

    Hukumar ba za ta ji kunya ba wajen sanya takunkumi ciki kuwa har da dakatarwa ko janye lasisi ko sanya kamfanin cikin jerin masu laifi ko cikin bakin littafi idan bukatar hakan ta taso.

    Hukumar ta NAHCON ta shawarci masu aniyar zuwa aikin Hajjin a bana da suka yi rijista da kamfanoni masu zaman kansu, su gaggauta bincikawa su tabbatar da ganin an shigar da bayanansu da yi masu rijista a tsarin na Nusuk kafin ranar 26 ga Satumba,2026 da ke zama cikar wa’adi.

    Wani abun muhimmi kuma da ya kamata a fahimta irin wannan cece-kuce bai cika tsayawa a wallafa labari guda daya ba, kasancewar akwai bukata ta kasuwanci, ana iya samun rahotanni a kafafan yada labarai da gabatar da takardar tuhuma da nacewa wajen bibiya da matsi daga al’umma duk ana gabatar da su a kokari na ganin mahukunta sun janye matsaya da suka kafu akanta ko a tsaya kan a bin aka fi cin moriya. Irin wannan ba bakon abu ba ne a bangaren da ake fafutka da ta shafi tattalin arziki, sai dai duk da haka kafewa da kin karbar canji bai kamata a mayar da shi hujja ba ta yin wani abu na kuskure.

    Takardar martanin hukumar ta NAHCON tace idan akwai wani abu da ake son a duba kan batun ba da kujerun Hajjin, ya kamata a gabatar da shi bisa hujja da bin ka’ida da hujjoji na hakika da bin hanyoyi na warware matsala ba kawai a rika gabatar da zargi ba kuma babu mai zargin, ko a rika kokari na bata suna.

    ‘Yan Najeriya na bukatar bayanai ne da aka samar bisa gaskiya da bin ka’ida da tantance hujja ba kawai a rika gina labarai ba kan zato da bacin rai ko zakuwa irin ta kasuwanci. Indai ba a ba da hujja ba komai na tsayawa ne a matakin na zargi kawai.

    NAHCON tace tana nan daram wajen yin aiki da gaskiya da daidaito da bin diddigi da lura da walwalar mahajjata, Hukumar ba za a raba mata hankali ba, da wata fafutuka ta wadanda ba a sani ko suwaye ba, ba za ta kuma bari ba sakaci na wasu kamfanoni masu jigila kalilan ya shafi irin kimar da Najeriya take da ita ba a fagen shirya aikin Hajji a idanun duniya.

    Read also: Kebbi Police Arrest 5 Suspects for Banditry, Reject ₦600,000 Bribe

    A karshe hukumar ta aikin Hajji a Najeriyar NAHCON ta nunar da cewa duk abin da za a fadi a kafa hujja da gaskiya da bin ka’ida da Saudiyya ke shimfidawa da abubuwan da ke biyo baya na ka’ida ba wai a tsara bayanai ba wadanda babu masu su ko ya zamana a rasa manufar yinsu.

    VON HAUSA

    #Hajj 2027 #Kujeru 5000 #NAHCON
    Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram WhatsApp

    Related Posts

    Ƴan Nijeriya na roƙon a rage wutar lantarki saboda firijinsu na daskarewa’

    September 17, 2026

    Bidiyon Wanka da Mata: Hisbah Ta Kama Fitaccen Ɗan TikTok

    September 17, 2026

    An rufe shagon maganin gargajiya na Kashiful Aleel

    September 12, 2026

    Harin Wuƙa: An Sallami Sheikh Lukuwa Daga Asibiti

    September 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Editors Picks

    NAHCON Ta Karyata Zargin Karkatar da Kujeru 5,000

    September 20, 2026

    KNSG Distributes 700 Fire Extinguishers to STSB Colleges

    September 20, 2026

    Speaker Commissions Development Projects in Zaria

    September 20, 2026

    KOMC Calls for Accuracy, Fairness in Election Reporting

    September 20, 2026
    • Facebook
    • YouTube
    • TikTok
    • WhatsApp
    Hajaj Albait 2
    © 2026 PARADIGM NEWS Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Home
    • About Us
    • Contact Us
    • Disclaimer
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.